Rundunar ’yan sanda a Jihar Kano ta sanar da cafke wani mutum da ke yi mata sojan-gona yana yaudarar jama’a domin karɓar musu kuɗi.
An cafke wanda ake zargin ne a ranar Lahadi, 21 ga Satumbar 2025 a yankin Kofar Dawanau, sanye da kayan ’yan sanda, wanda bayanai suka ce ya daɗe yana aika-aikar.
An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno Sanata Natasha ta koma Majalisar DattawaSanawar da rundunar ta fitar ta bayyana cewe an kama shi ne bayan da jama’a suka shigar da ƙorafe-ƙorafe da dama game da ayyukan wasu da ke yin kutse da shigar ’yan sanda domin damfarar jama’a.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce “binciken farko ya tabbatar cewa wanda ake zargin ba ɗan sanda ba ne, kuma ba shi da alaƙa da rundunar kwata-kwata.”
A wata hira da rundunar ta yi da mutumin wanda mazaunin Kofar Waika ne, ya ce sha’awar aikin ce ta sanya yake yi wa ’yan sandan sojan gona, inda yake bayar da hannu a kan titi domin samun na ɓatarwa.
Ya shaida cewa shaye-shayen da yake yi bai wuce na sigari da tabar wiwi ba, inda ya nemi a yi masa afuwa duk da ya nanata cewa duk duniya babu aikin da yake sha’awa kamar aikin ’yan sanda tare da neman a taimaka a dauke shi aikin.
Kazalika, ya bayyana cewa muradin ganin ya zama ɗan ya sanya shi sake aikata wannan laifi na sojan-gona duk da an taɓa kama shi da laifin a baya.
Tuni dai rundunar ta bayyana cewa za a gurfanar da shi a gaban kotu domin fuskantar hukunci bayan kammala bincike.
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai ko ƙorafe-ƙorafe idan sun san wani abu game da wanda ake zargi ko makamantansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
A cewar ‘yansanda, “A ranar 10/10/25, an gayyato wani Mista Oke Emmanuel, dan NYSC kuma abokin dakin wanda ya bace, domin yi masa tambayoyi. Ya tabbatar cewa wanda ake nema ya kasance tare da iyalan George har zuwa 06/10/25.
“An samu karin bayani daga George cewa dan NYSC din ya koka da rashin lafiya, aka kai su Asibitin Kaiama Referral Hospital a ranar 04/10/25, kuma aka sallame shi ranar 05/10/25. Sai dai a ranar 06/10/25, dan NYSC din ya bace zuwa wani wurin da ba a sani ba.”
‘Yansanda kuma suna binciken zargin karbar kudin rashawa na Naira 100,000 daga iyayen wanda ya bace, da wasu fursunoni biyu da ke gidan gyaran hali na Igbara, Abeokuta, Jihar Ogun, wadanda suka yi suna kamar masu garkuwa da mutane.
“An bar wayar salula ta wanda ya bace a dakinsa. Jami’an bincike suka bi layin kira daga lambar 0906193291, inda aka gano tana hannun wani fursuna da ake tsare da shi a cibiyar gyaran hali ta Igbara, Abeokuta, saboda wani laifin garkuwa da mutane.
“Wanda ake zargin ya ce sun ga lambar wayar a kafafen sada zumunta, suka yi amfani da ita don cutar da mahaifin wanda ya bace, Mista Anyanwu Simon, mai shekara 56. An biya kudin Naira 100,000 zuwa asusun Opay mai lamba 7042793493 na wata Atinuke Oluwalose, abokiyar hadin bakin fursunan da ke gidan yarin Abeokuta.”
“Daga bayanan da jami’an bincike suka gano, akwai wasu abubuwan damuwa da ka iya kasancewa silar abin da ya faru. An gano wasu kalaman da wanda ya bace ya yi dangane da wasu sabbin dabi’u da sha’awowi da ba su dace da akidar addininsa ba,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta kammala da cewa ana ci gaba da daukar matakan bincike “domin tabbatar da sakamakon da jami’an bincike suka tattara, kasancewar binciken ya fito da abubuwa masu ban mamaki. Ba a samu wata alamar garkuwa da mutane a wannan lamari ba. Ana ci gaba da aiki domin samun cikakken bincike.”
PUNCH Metro ta ruwaito a watan Oktoba 2024 cewa an kama mutum hudu kan bacewar wani dan NYSC mai suna Yahya Faruk, wanda yake hidima a Ikuru, cikin Karamar Hukumar Andoni ta jihar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA