Aminiya:
2025-09-24@08:31:55 GMT

An kama ɗan sandan bogi a Kano

Published: 24th, September 2025 GMT

Rundunar ’yan sanda a Jihar Kano ta sanar da cafke wani mutum da ke yi mata sojan-gona yana yaudarar jama’a domin karɓar musu kuɗi.

An cafke wanda ake zargin ne a ranar Lahadi, 21 ga Satumbar 2025 a yankin Kofar Dawanau, sanye da kayan ’yan sanda, wanda bayanai suka ce ya daɗe yana aika-aikar.

An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa

Sanawar da rundunar ta fitar ta bayyana cewe an kama shi ne bayan da jama’a suka shigar da ƙorafe-ƙorafe da dama game da ayyukan wasu da ke yin kutse da shigar ’yan sanda domin damfarar jama’a.

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce “binciken farko ya tabbatar cewa wanda ake zargin ba ɗan sanda ba ne, kuma ba shi da alaƙa da rundunar kwata-kwata.”

A wata hira da rundunar ta yi da mutumin wanda mazaunin Kofar Waika ne, ya ce sha’awar aikin ce ta sanya yake yi wa ’yan sandan sojan gona, inda yake bayar da hannu a kan titi domin samun na ɓatarwa.

Ya shaida cewa shaye-shayen da yake yi bai wuce na sigari da tabar wiwi ba, inda ya nemi a yi masa afuwa duk da ya nanata cewa duk duniya babu aikin da yake sha’awa kamar aikin ’yan sanda tare da neman a taimaka a dauke shi aikin.

Kazalika, ya bayyana cewa muradin ganin ya zama ɗan ya sanya shi sake aikata wannan laifi na sojan-gona duk da an taɓa kama shi da laifin a baya.

Tuni dai rundunar ta bayyana cewa za a gurfanar da shi a gaban kotu domin fuskantar hukunci bayan kammala bincike.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai ko ƙorafe-ƙorafe idan sun san wani abu game da wanda ake zargi ko makamantansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

An sanya tukwicin N10m domin kama makasan limamin coci a Enugu

Gwamnatin Jihar Enugu ta tanadi tukwuicin naira miliyan goma ga duk mutumin da ya taimaka aka kama waɗanda ake zargi da kashe fitaccen limamin cocin Katolika, Matthew Eya.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa tabbatar da alƙawari da Kwamishinan Labarai, Malachy Agbo, ya fitar ranar a Asabar.

NAF ta hallaka Boko Haram 32 a Borno Jami’ar European-American ta musanta bai wa Rarara digirin girmamawa

Wasu ‘yan bindiga ne suka harbe Mr Eya, limamin cocin katolika ta Saint Charles Catholic Church da ke garin Eha-Ndiagu ranar Juma’a a kan hanyar Eha-Alumonah–Eha-Ndiagu da ke ƙaramar hukumar Nsukka.

Rahotanni sun ce ’yan bindiga sun yi wa limamin kwanton-ɓauna wanda suke harbe a yayin da yake kan hanyar komawa gida daga yankin Enugu Urban.

Limamin cocin mamba ne a Cocin Nsukka Catholic Diocese, wadda ta tabbatar da kisan nasa.

A sanarwar da Mista Agbo ya fitar, ya ambato gwamnatin Enugu tana “yin Allah wadai da kakkausar muryar” bisa “mummunan kisan” da aka yi wa limanin cocin.

“Gwamnatin Enugu tana miƙa saƙon ta’aziyyarta ga iyalan limanin cocin, da Catholic Diocese ta Nsukka, da kuma mabiya ɗarikar Katolika baki ɗaya bisa wannan iftila’i,” a cewar kwamishinan.

Ya bayyana makasan a matsayin “matsorata” waɗanda suka aiwatar da kisan “rashin imani”, inda ya sha alwashin cewa gwamnati za ta kama ‘yan bindigar da suka yi wannan aika-aika.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Ɗansandan Bogi A Kano
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno
  • An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina
  • An sanya tukwicin N10m domin kama makasan limamin coci a Enugu