Aminiya:
2025-11-08@11:13:28 GMT

Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya

Published: 21st, September 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bar Abuja zuwa birnin New York na Ƙasar Amurka, domin halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80.

Taron zai gudana daga ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, zuwa ranar Lahadi, 28 ga watan Satumba, 2025.

Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu Jami’ar European-American ta musanta bai wa Rarara digirin girmamawa

Shettima zai wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wannan babban taro.

Zai gabatar da jawabi, tare da shiga muhawarar shugabannin ƙasashe a zauren taron.

A yayin taron, Mataimakin Shugaban zai kuma bayyana sabbin muradun Najeriya a ƙarƙashin yarjejeniyar kare muhalli.

Wannan zai gudana ne a wani taro na musamman kan sauyin yanayi da Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya zai shirya a ranar Laraba, 24 ga watan Satumba.

Haka kuma, Shettima zai halarci wani taron koli kan samar da gidaje masu sauƙi da sauƙin farashi, wanda Shugaban Ƙasar Kenya zai jagoranta.

Bayan kammala taron, Shettima zai wuce Birnin Frankfurt, na Ƙasar Jamus, inda zai gana da jami’an bankin Deutsche Bank kafin dawowa Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya taro Tattauanawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

 

Bugu da kari, Amurka ta bayyana a fili cewa batun sauyin yanayi shi ne mafi girman yaudara da aka yi a tarihin dan Adam, kuma ta fice daga “Yarjejeniyar Paris” sau biyu, wanda hakan ya yi mummunar illa ga kokarin al’ummun duniya na kyautata yanayin duniya, kana ta zama babban cikas ga hadin gwiwar duniya a fannin magance sauyin yanayi.

 

Geng Shuang ya kuma bayyana cewa, a kan batun magance sauyin yanayi, abun da al’ummar duniya ke bukata shi ne dunkulewa da hadin gwiwa, ba zargi da dora laifi kan wasu ba. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil November 7, 2025 Daga Birnin Sin An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo November 7, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta November 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nigeria: Za A Ci Gaba Da Zaman Shari’ar Shugaban Kungiyar “IPOB” A ranar 20 Ga Watan Nan Na Nuwamba
  • Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • Za a gudanar da wasannin ƙwallon yashi a Abuja