CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI
Published: 22nd, September 2025 GMT
Hukumar da ke kula da yi wa Kamfanoni Rajista ta Najeriya (CAC) ta ƙaddamar da sabon shafin intanet mai amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira wato AI domin sauƙaƙa rajistar harkokin kasuwanci da kamfanoni a Najeriya.
Shugaban Hukumar, Hussaini Ishaq Magaji (SAN), ne ya bayyana a yayin taron masu ruwa da tsaki da hukumar ta shirya a Kano ranar Litinin.
Ya kuma ce hukumar ta kawo sabbin sauye-sauye da za su inganta ayyukanta da kuma sauƙaƙa wa ’yan kasuwa yin rajista da ita.
Magaji ya ce, “Ko ina kake, daga dakinka, ba tare da ka san kowa a CAC ba, kuma ba tare da biyan kowa komai ba, za ka iya yin rajistar sunan kasuwancinka ka samu takardar shaidarka cikin ƙasa da minti 10.”
“Adadin bayanan da shafinmu na intanet ke ɗauka ya tashi daga 3.5TB zuwa kusan 12TB cikin watanni uku da fara jagorancin hukumar,” in ji shi.
Shugaban ya kuma ce hukumar na karɓar saƙon imel sama da 3,000 a kullum, yayin da ma’aikata ƙasa da 100 ke kula da su da kuma bayar da amsa.
Sai dai ya ce sabon shafin da aka ƙaddamar, zai karanta kuma ya rarraba tare da bayar da amsa ga dubban sakonnin na imel cikin daƙiƙa daya.
Ya kuma ce karfin aikin shafin wanda aka fara amfani da shi a watan Yuni ba shi da iyaka.
Hussaini ya ce, “Babu inda a duniya ake yin rajistar sunan kasuwanci cikin ƙasa da minti 10. Mu ne muka fara, sauran su biyo baya.
“A yau kaɗai, akwai aƙalla kamfanoni 7,000 da ke buƙatar a yi musu rijista, yayin da ma’aikata 63 ne kawai ke aikin. Wannan ne ya sa dole mu fara amfani da wannan fasahar domin inganta ayyukanmu,” in ji shi.
Ana sa ran shugaban hukumar zai gabatar da jawabi kan nasarorin da hukumar ta samu a fasahar a yayin taron hukumomin da ke kula da yi wa kamfanoni rajista na duniya da za a yi a ƙasar Tunisia wata mai zuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Kasuwanci
এছাড়াও পড়ুন:
Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
Wani jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa a yayin da take guje wa harin ’yan bindiga a kauyen Allawa da ke Karamar Hukumar Shiroro a Jihar Neja.
Sarkin yankin Bassa, Bagudu Amos, ne ya bayyana hakan a lokacin taron tattaunawa da mata kan zaman lafiya da kare su daga cin zarafi, mai taken: “Ƙarfafa kariya daga cin zarafin jima’i da na jinsi a Jihar Neja.”
Kungiyar Tunani Initiative, tare da goyon bayan Dorothy Njemanze Foundation da Ford Foundation, ce ta shirya taron domin ƙarfafa mata wajen yaki da cin zarafi da ke ƙara ta’azzara a sakamakon rashin tsaro.
Bagudu Amos ya bayyana cewa mahaifiyar ta yi tafiya mai nisa a kafa da jaririn a bayanta domin tserewa daga harin ’yan bindiga, amma daga bisani ta gano cewa jaririn ya riga ya mutu a bayanta.
Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen MalabuYa ce lamarin da ya faru a shekarar 2023, na ɗaya daga cikin dimbin abubuwan firgici da mata ’yan gudun hijira ke fuskanta a kullum, inda mafi yawansu ba su da isasshen tallafi ko ƙarfafa gwiwa wajen yaki da cin zarafin jinsi da ke biyo bayan matsalar tsaro.
Shugabar Tunani Initiative, Maryam Mairo Ibrahim, ta nuna damuwarta kan yadda ba a ba wa mata muhimmanci da ya dace wajen shiga cikin harkar sasanta rikice-rikice da zaman lafiya a Jihar Neja. Ta yi kira ga mata da su haɗa kai domin karya shingayen da ke hana su shiga harkokin warware rikice-rikice.
“A Jihar Neja, kamar yadda ake gani a wasu wuraren da ke fama da rashin tsaro, mata su ne mafiya fuskantar ƙuncin hare-haren ’yan bindiga. Idan an kai hari, mafi yawanci maza ake kashewa, sai a bar mata da nauyin sake gina iyali daga farko. Wannan rawar da mata ke takawa ba a ba shi muhimmancin da ya kamata. Wannan shi ne dalilin da ya sa taron ya mayar da hankali kan ƙara bayyana muhimmancin mata a harkar zaman lafiya da kuma yaki da cin zarafi,” in ji ta.
Daraktan Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam a Jihar Neja, Ambasada Nuhu Muhammad, ya jaddada muhimmancin samun karin mata a majalisar dokokin jiha da ma ta ƙasa domin samar da dokoki da manufofi da za su amfanar da su.
Mata da suka halarci taron sun yi kira da a tsaurara hukunci kan masu yi wa mata fyade, tare da kira da a haɗa ƙarfi da ƙarfafa juna wajen shawo kan yawaitar cin zarafi musamman a ƙauyuka.
Mahalarta sun kuma jaddada muhimmancin kafa ƙungiyar mata mai ƙarfi guda ɗaya domin tunkarar matsalar cin zarafin mata a Jihar Neja.