NAF ta hallaka Boko Haram 32 a Borno
Published: 21st, September 2025 GMT
Rundunar Sojin Saman Najeriya, ta kashe ’yan ta’addan Boko Haram 32, a wani farmaki da ta kai garin Banki da ke Ƙaramar Hukumar Bama, a Jihar Borno.
Rahoton ya bayyana cewa farmakin ya auku ne a ranar 18 ga watan Satumba da misalin ƙarfe 10:15 na safe.
Bayan biyan N50m an sako ma’aurata da ’yarsu su da aka sace a Katsina Mutum 9 sun rasu a hatsarin jirgin ruwa a SakkwatoWannan na zuwa ne bayan ’yan ta’addan sun kai hari hedikwatar ’yan sanda da ke Banki.
A lokacin kai farmaki , sojoji biyu sun rasa rayukansu, haka kuma wani ƙaramin yaro mai shekara tara, Ismail Abubakar, ya rasu.
Har ila yau, maharan sun ƙone motocin soja uku.
Bayan kai harin, sojin sama na Operation Had6in Kai sun tura jirgin A-29 Super Tucano wanda ya yi wa ’yan ta’addan ruwan wuta.
Wannan ya janyo mahara 32 sun mutu sakamakon ɓarin wuta da suka sha.
An kwashe gawar sojojin zuwa Maiduguri, yayin da aka miƙa wa iyayen yaron gawarsa domin yi masa sutura.
Daga ƙarshe, an ƙara tura jami’an tsaro zuwa Banki domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Farmaki hari
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta yi Watsi Da Batun Tura Sojojin Kasashen Waje Zuwa Gaza
Rahotanni sun nuna cewa shugaban kungiyar gwagwarmaya ta Hamas Musa abu marzuk ya shaidawa gidan talabijin din Aljazeera cewa sun yi watsi da batun tura dakarun tabbatar da zaman lafiya zuwa yankin Gaza wadanda zasu yi aiki a madadin sojojin mamayar Isra’ila
Yace ba zamu taba amincewa da aikewa da sojojin da za su zama madadin sojojin Isra’ila a gaza ba,
Wannan bayanin ya zo ne bayan da kasar Amurka ta fitar da wani daftarin kuduri a kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya dake bukatar kafa dakarun tababtar da zaman lafiya na wucin gadi a yankin Gaza, akalla na shekaru 2 adaidai lokacin da falasdinawa ke fargabar tsoma bakin kasashen waje a yankin,
Rahotanni da aka fitar ya nuna cewa kasashen Amurka, Turkiya, Qatar da kasar Masar ne za su kafa dakarun tabbatar da zaman lafiya a Gaza, kasashen da suka jagorancin tattaunawar dakatar da bude wuta tsakanin isra’ila da Hamas tun a watan daya gabata
Ana sa bangaren Musa Abu Marzuk ya kara da cewa zai zama lamari ne mai wahalar gaske kwamitin tsaron na majalisar dinkin duniya ya kafa dakarun tabbatar da zaman lafiya na majalisar a yankin Gaza kamar yadda Amurka ta tsara.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Da Pakistan Sun Kulla Yarjeniyoyi Guda Biyar Kan Harkar Sadarwa Da Al’adu November 5, 2025 Ansarullah: Dakarunsu A Shirye Suke Don Tunkarar Duk Wata Barazana Daga Isra’ila November 5, 2025 Shugaban Najeriya Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU November 5, 2025 Kakakin Dakarun IRGC Ya Ce; Ko Kadan Amurka Ba Abar Amincewa Ba Ce November 4, 2025 Admiral Sayyari Ya Ce: Isra’ila Ba Ta Kai Matsayin Da Zata Yaki Iran Ba November 4, 2025 Kakakin Majalisar Dokokin Lebanon Ya Jaddada Gagarumin Tsaron Kasa Da Gwagwarmaya Ta Baiwa Lebanon November 4, 2025 Mataimakin Tsohon Shugaban Kasar Amurka Dick Cheney Ya Mutu A Yau Talata November 4, 2025 Ana Tattara Gawawwakin Mutanen Da Mayakan Rapid Support Forces Suka Kashe A Arewacin Kordofan Na Sudan November 4, 2025 Iran : Jagora ya gindaya wasu sharudda kafin yin duk wata hulda da Amurka November 4, 2025 Kasashen Musulmi : Falasdinawa ne kadai ke da hakkin jagorantar yankinsu November 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci