Aminiya:
2025-11-05@08:42:17 GMT

NAF ta hallaka Boko Haram 32 a Borno

Published: 21st, September 2025 GMT

Rundunar Sojin Saman Najeriya, ta kashe ’yan ta’addan Boko Haram 32, a wani farmaki da ta kai garin Banki da ke Ƙaramar Hukumar Bama, a Jihar Borno.

Rahoton ya bayyana cewa farmakin ya auku ne a ranar 18 ga watan Satumba da misalin ƙarfe 10:15 na safe.

Bayan biyan N50m an sako ma’aurata da ’yarsu su da aka sace a Katsina Mutum 9 sun rasu a hatsarin jirgin ruwa a Sakkwato

Wannan na zuwa ne bayan ’yan ta’addan sun kai hari hedikwatar ’yan sanda da ke Banki.

A lokacin kai farmaki , sojoji biyu sun rasa rayukansu, haka kuma wani ƙaramin yaro mai shekara tara, Ismail Abubakar, ya rasu.

Har ila yau, maharan sun ƙone motocin soja uku.

Bayan kai harin, sojin sama na Operation Had6in Kai sun tura jirgin A-29 Super Tucano wanda ya yi wa ’yan ta’addan ruwan wuta.

Wannan ya janyo mahara 32 sun mutu sakamakon ɓarin wuta da suka sha.

An kwashe gawar sojojin zuwa Maiduguri, yayin da aka miƙa wa iyayen yaron gawarsa domin yi masa sutura.

Daga ƙarshe, an ƙara tura jami’an tsaro zuwa Banki domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Farmaki hari

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta yi Watsi Da Batun Tura Sojojin Kasashen Waje Zuwa Gaza

Rahotanni sun nuna cewa shugaban kungiyar gwagwarmaya ta Hamas Musa abu marzuk ya shaidawa gidan talabijin din Aljazeera cewa  sun yi watsi da batun tura dakarun tabbatar da zaman lafiya zuwa yankin Gaza wadanda zasu yi aiki a madadin sojojin mamayar Isra’ila

Yace ba zamu taba amincewa da aikewa da sojojin da za su zama madadin sojojin Isra’ila a gaza ba,

Wannan bayanin ya zo ne bayan da kasar Amurka ta fitar da wani daftarin kuduri a kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya dake bukatar kafa dakarun tababtar da zaman lafiya na wucin gadi a yankin Gaza, akalla na shekaru 2 adaidai lokacin da falasdinawa ke fargabar tsoma bakin kasashen waje a yankin,

Rahotanni da aka fitar ya nuna cewa kasashen Amurka, Turkiya, Qatar da kasar Masar ne za su kafa dakarun tabbatar da zaman lafiya a Gaza, kasashen da suka jagorancin tattaunawar dakatar da bude wuta tsakanin isra’ila da Hamas tun a watan daya gabata

Ana sa bangaren Musa Abu Marzuk ya kara da cewa zai zama lamari ne mai wahalar gaske kwamitin tsaron na majalisar dinkin duniya ya kafa dakarun tabbatar da zaman lafiya na majalisar a yankin Gaza kamar yadda Amurka ta tsara.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Da Pakistan Sun Kulla Yarjeniyoyi Guda Biyar Kan Harkar Sadarwa Da Al’adu November 5, 2025  Ansarullah: Dakarunsu A Shirye Suke Don Tunkarar Duk Wata Barazana Daga Isra’ila November 5, 2025 Shugaban Najeriya Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU November 5, 2025 Kakakin Dakarun IRGC Ya Ce; Ko Kadan Amurka Ba Abar Amincewa Ba Ce November 4, 2025 Admiral Sayyari Ya Ce: Isra’ila Ba Ta Kai Matsayin Da Zata Yaki Iran Ba November 4, 2025 Kakakin Majalisar Dokokin Lebanon Ya Jaddada Gagarumin Tsaron Kasa Da Gwagwarmaya Ta Baiwa Lebanon November 4, 2025 Mataimakin Tsohon Shugaban Kasar Amurka Dick Cheney Ya Mutu A Yau Talata November 4, 2025 Ana Tattara Gawawwakin Mutanen Da Mayakan Rapid Support Forces Suka Kashe A Arewacin Kordofan Na Sudan November 4, 2025 Iran : Jagora ya gindaya wasu sharudda kafin yin duk wata hulda da Amurka    November 4, 2025 Kasashen Musulmi : Falasdinawa ne kadai ke da hakkin jagorantar yankinsu November 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Ga Wani Dan Majalisa A Jihar Niger
  • Hamas Ta yi Watsi Da Batun Tura Sojojin Kasashen Waje Zuwa Gaza
  • Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
  • Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
  • Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mulki na biyu a Tanzaniya
  • An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mullki na biyu a Tanzaniya
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • An kashe ’yan bindiga 19 yayin wani hari a Kano
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka