Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin
Published: 19th, September 2025 GMT
Albarkacin bikin murnar cika shekaru 100 na kafuwar Jam’iyyar Zhigong ta Sin, shugaban kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta Sin, JKS, kana shugaban kasar Xi Jinping ya aika wasikar taya murna, kuma a madadin kwamitin tsakiyar JKS, ya taya dukkan ’yan Jam’iyyar Zhigong murna tare da nuna musu gaisuwa.
Xi Jinping ya jaddada cewa, a kan sabon tafarki, ana fatan Jam’iyyar Zhigong ta ci gaba da zaune bisa jagorancin JKS, ta kuma kara zurfafa fahimta da aiwatar da tsarin gurguzu mai sigar musamman na kasar Sin, ta hada kai da ’yan uwa Sinawa dake ketare, da wadanda suka dawo gida, da kuma daliban dake karatu a kasashen waje, don ba da gudunmawa ga babban aikin dunkulewar kasar, da kuma taka rawar gani ga aikin gina kasa mai karfi ta hanyar zamanintar da al’umma da kuma farfado da al’umma.
An gudanar da babban bikin murnar cika shekaru 100 na kafuwar Jam’iyyar Zhigong ta Sin a yau Juma’a 19 ga wata a nan birnin Beijing. shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin siyasa na Sin Wang Hu’ning ya halarci taron tare da gabatar da jawabi. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Jam iyyar Zhigong ta
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu Ta Yi Kira Ga Zaman Lafiya A Duniya
Uwargidan shugaban kasar Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira da a kara fahimtar juna a tsakanin kasashe tare da yin addu’ar samun zaman lafiya a duniya a yayin da ake fama da rikice-rikice a duniya.
Ta yi wannan kiran ne a lokacin da ta karbi bakuncin jakadan Qatar a Najeriya Ali bin Ghanem Al-Hajri a ofishinta da ke Abuja. Uwargidan shugaban kasar, yayin da take mayar da jawabi game da harin da aka kai a birnin Doha na baya-bayan nan, ta jaddada cewa, zaman lafiya, kamar yadda manyan addinai ke wa’azi, muhimmin abu ne ga bil’adama, kuma ya kamata ya kasance muhimmin fifiko ga dukkan kasashe.
Tattaunawar da aka yi a yayin ziyarar, wadda ta kasance a bayan kofofin yada labarai, ta mayar da hankali ne kan karfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyar Renewed Hope Initiative da kungiyar Qatar Foundation for Education, Science and Development Community. Bangarorin biyu sun yi nazari kan bangarorin hadin gwiwa, musamman wajen inganta tsarin karatun Almajiri da kuma tinkarar kalubalen yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya.
Ambasada Al-Hajri ya bayyana godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar da al’ummar Najeriya bisa hadin kai da kuma kiran da suke yi na samar da zaman lafiya a duniya, inda ya ce Najeriya ta kasance amintacciyar abokiyar hulda da kasar Qatar.
Bello Wakili