Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
Published: 22nd, September 2025 GMT
Wani jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa a yayin da take guje wa harin ’yan bindiga a kauyen Allawa da ke Karamar Hukumar Shiroro a Jihar Neja.
Sarkin yankin Bassa, Bagudu Amos, ne ya bayyana hakan a lokacin taron tattaunawa da mata kan zaman lafiya da kare su daga cin zarafi, mai taken: “Ƙarfafa kariya daga cin zarafin jima’i da na jinsi a Jihar Neja.
Kungiyar Tunani Initiative, tare da goyon bayan Dorothy Njemanze Foundation da Ford Foundation, ce ta shirya taron domin ƙarfafa mata wajen yaki da cin zarafi da ke ƙara ta’azzara a sakamakon rashin tsaro.
Bagudu Amos ya bayyana cewa mahaifiyar ta yi tafiya mai nisa a kafa da jaririn a bayanta domin tserewa daga harin ’yan bindiga, amma daga bisani ta gano cewa jaririn ya riga ya mutu a bayanta.
Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen MalabuYa ce lamarin da ya faru a shekarar 2023, na ɗaya daga cikin dimbin abubuwan firgici da mata ’yan gudun hijira ke fuskanta a kullum, inda mafi yawansu ba su da isasshen tallafi ko ƙarfafa gwiwa wajen yaki da cin zarafin jinsi da ke biyo bayan matsalar tsaro.
Shugabar Tunani Initiative, Maryam Mairo Ibrahim, ta nuna damuwarta kan yadda ba a ba wa mata muhimmanci da ya dace wajen shiga cikin harkar sasanta rikice-rikice da zaman lafiya a Jihar Neja. Ta yi kira ga mata da su haɗa kai domin karya shingayen da ke hana su shiga harkokin warware rikice-rikice.
“A Jihar Neja, kamar yadda ake gani a wasu wuraren da ke fama da rashin tsaro, mata su ne mafiya fuskantar ƙuncin hare-haren ’yan bindiga. Idan an kai hari, mafi yawanci maza ake kashewa, sai a bar mata da nauyin sake gina iyali daga farko. Wannan rawar da mata ke takawa ba a ba shi muhimmancin da ya kamata. Wannan shi ne dalilin da ya sa taron ya mayar da hankali kan ƙara bayyana muhimmancin mata a harkar zaman lafiya da kuma yaki da cin zarafi,” in ji ta.
Daraktan Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam a Jihar Neja, Ambasada Nuhu Muhammad, ya jaddada muhimmancin samun karin mata a majalisar dokokin jiha da ma ta ƙasa domin samar da dokoki da manufofi da za su amfanar da su.
Mata da suka halarci taron sun yi kira da a tsaurara hukunci kan masu yi wa mata fyade, tare da kira da a haɗa ƙarfi da ƙarfafa juna wajen shawo kan yawaitar cin zarafi musamman a ƙauyuka.
Mahalarta sun kuma jaddada muhimmancin kafa ƙungiyar mata mai ƙarfi guda ɗaya domin tunkarar matsalar cin zarafin mata a Jihar Neja.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jariri Tsaro a Jihar Neja yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai
Majalisar Tarayya ta amince da hukuncin cin sarƙa ga duk wani malami da aka samu da laifin cin zarafi ko lalata da ɗalibai a makarantu a faɗin ƙasar nan.
Hakan ya biyo bayan amincewar majalisar da Dokar Hana Lalata da Dalibai ta 2025 (HB.1597), bayan tsallake karatu na uku a Majalisar Dattawa da kuma Majalisar Wakilai a ranar Laraba.
Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a JosA ƙunshin bayanan da dokar, za a iya yanke wa duk wanda ya saɓa mata hukuncin ɗaurin shekara 14 ko shekara biyar mafi ƙaranci ba tare da zaɓin biyan tara ba.
Laifukan da dokar ta bayyana a matsayin cin zarafi sun haɗa da yin jima’i ko neman wata alfarma daga ɗalibai a madadin jima’i, barazana, ko tozartarwa da ɗaga hankali a wajen karatu, ko taɓawa ko rungumar jiki.
Haka kuma dokar ta haɗa da aika saƙonnin batsa, hotuna ko bidiyo, ko barkwanci ko magana mai ɗauke da cin zarafi kan jikin ɗalibi, da kuma bibiya da sa ido mai tsanani.
Sabuwar dokar, wadda ke jiran sahalewar shugaban ƙasa kafin ta fara aiki, ta bai wa waɗanda abin ya shafa damar shigar da ƙarar malamin da ya aikata laifin na cin amana.
Haka kuma dokar ta wajabta wa duk makarantu na gaba da sakandare su kafa kwamitin musamman mai zaman kansa domin kula da korafe-korafe da suka shafi cin zarafi, a bisa tsarin doka.
Dokar ta ce ba za a ɗauki yarda daga ɗalibi a matsayin hujja ta kare kai ba, sai idan ɓangarorin biyu sun yi aure bisa doka. Ta kuma bayyana cewa ba sai an tabbatar da niyyar cin zarafi ba kafin a samu hukunci.
Haka zalika, ta haramta wa makarantu gudanar da bincike na cikin gida idan an riga an kai ƙara kotu, inda ta ce har sai an gama shari’ar kafin su iya shiga tsakani.
Dokar ta kuma bai wa ɗalibai, ’yan uwa, wali ko lauya damar kai ƙara, tare da ba da damar miƙa rahoto ga rundunar ‘yan sanda ko ofishin Antoni-Janar, sannan a tura kwafin ƙarar ga kwamitin hana cin zarafi na makarantar da abin ya shafa.