Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
Published: 22nd, September 2025 GMT
Dangane da halin da ake ciki game da rikicin Falasdinu da Isra’ila, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin 22 ga wata cewa, karfin soja ba zai iya samar da zaman lafiya ba, kuma tashin hankali ba zai iya samar da tsaro ba. Kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashen duniya wajen ci gaba da jajircewa a kan tsagaita bude wuta da kawo karshen yakin da ake yi a zirin Gaza, da kuma matukar nuna goyon baya ga tabbatar da adalci ga al’ummar Falasdinawa wajen maido da hakkinsu na kasa, da kuma kara azamar warware matsalar Falasdinu tun da wuri ta hanyar samar da cikakkiyar mafita, mai adalci da kuma dorewa.
Guo Jiakun ya ce, kawo karshen rikicin cikin hanzari da samar da dawwamammen zaman lafiya, shi ne babban burin al’ummar Falasdinu da Isra’ila da kuma yankin Gabas ta Tsakiya, kuma wannan aiki ne na gaggawa da ke gaban kasashen duniya. Kasar Sin ta yi imanin cewa, a halin da ake ciki yanzu, ya zama tilas a karfafa tsagaita bude wuta a zirin Gaza, tare da daukar matakin gaggawa domin rage radadin bala’in jin kai a yankin.
Ya ci gaba da cewa, ya kamata kasashen da ke da tasiri na musamman a kan Isra’ila su sauke nauyin da ke wuyansu. Dole ne a aiwatar da ka’idar barin “Falasdinawa su mulki Falasdinu” bisa turbar gaskiya, kuma dole ne a kiyaye hakkin kasar Falasdinu kan batutuwan da suka shafi shugabanci bayan yaki da kuma shirye-shiryen sake gina kasar. Kazalika, a cewarsa, dole ne a ci gaba da bibiyar shawarar “kafa kasashe biyu” ba tare da kakkautawa ba, da samar da karin fahimtar juna da cimma matsaya tsakanin kasa da kasa da kuma yin watsi da duk wani mataki na bangare guda da zai iya yin kafar ungulu a kan “kafuwar kasashe biyu”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta ce a karon farko za ta shirya taron zuba jari da samar da masana’antu na Arewacin Najeriya, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 29 da 30 ga watan Satumba a Abuja.
Taron wanda aka shirya tare da hadin gwiwar jihohin arewa 19 da kuma kamfanin raya yankin – NNDC, na da nufin mayar da yankin a matsayin wata cibiya ta samun bunkasar tattalin arziki da habaka masana’antu.
An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AIDa yake magana a taron manema labarai da aka gudanar ranar Litinin a Abuja, kakakin kungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya bayyana taron a matsayin “kira domin zaburar da tattalin arziki da kuma tsare-tsare na cika alkawarin Arewacin Najeriya.”
Ya ce an tsara taron ne a cikin watanni 18 da suka gabata domin kaddamar da wani shiri na kishin kasa wanda zai karfafa ayyukan ci gaba da bude sabbin kafofin damammanki ga yankin, Najeriya da abokan huldar kasa da kasa.
“Wannan taron ba na siyasa ba ne, yana mai da hankali kan tattalin arziki, kan damammaki, da kuma samar da wadata. Yana da zimmar nuna karfin Arewacin Najeriya da kuma gabatar da hangen nesa na ci gaba, kirkire-kirkire, da haɗin gwiwa. Daga yau, za mu bude sabon babi,” in ji Jiddere.
Da yake yin la’akari da irin gudunmawar da yankin ya bayar a tarihi, ya tuna cewa a shekarun 1960 zuwa farkon 1980, Arewacin Nijeriya ya ba da karfin tattalin arzikin kasa ta hanyar noma, masana’antu, da kasuwanci. “Dalarmu na gyada ya kai sararin sama; auduga, fatu, dabbobi, da ma’adanai masu ƙarfi suna tallafawa masana’antu,” in ji shi.
Duk da haka, ya ce rashin tsaro da rashin zuba jari sun rage ci gaban yankin, wanda ya haifar da rikice-rikice na albarkatu masu yawa da kuma abubuwan da ba a san su ba, “Wannan taron yana manufa juya akalar rikicin zuwa ga damammaki da kuma tabbatar da cewa Arewacin Najeriya ya samu kwarin gwiwa zuwa wani sabon zamani na ci gaba,” in ji shi.
Jiddere ya zayyana ginshiƙai masu mahimmanci guda biyar da yankin yake tutiya da su kamar albarkar ƙasa da noma, manyan ma’adanai, albarkatun ɗan adam, ababen more rayuwa, da masana’antu, waɗanda ke samun tallafi kamar ilimi, kiwon lafiya, gidaje, da fasaha.
Ya nanata cewa Arewacin Najeriya “yana da alaƙa da kasa-wata babbar hanyar shiga Nijar, Chadi, Kamaru, Benin, Mali, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.”
Ya ƙalubalanci masu ruwa da tsaki da su yi nazari a kan abubuwan da ba za a iya amfani da su a yankin ba, yana mai tambaya, “Ta yaya yankin da ya samar da shugabanni da masu ƙirkire-ƙirkire a duniya, ’yan ƙato da gora irin su Alhaji Aliko Dangote da Amina Mohammed, har yanzu bai nuna cikakken ƙarfin tattalin arzikinsa ba?