Aminiya:
2025-11-04@14:51:43 GMT

An tsinci gawar kwamandan hukumar NDLEA a otel a Kalaba

Published: 20th, September 2025 GMT

An tsinci gawar Igbonna Uzoma, kwamandan hukumar da ke yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) a otel da ke birnin Kalaba, Jihar Kuros Riba, a ranar Juma’a.

Rahotanni sun ce Uzoma, wanda aka dawo da shi aiki daga wata jiha zuwa Kuros Riba a kwanan nan, bai daɗe da kama aiki a sabon ofishin ba kafin wannan lamarin da ya jefa hukumar cikin ɗimuwa.

Kakakin NDLEA na ƙasa, Femi Babafemi, ya tabbatar da mutuwar babban jami’in, inda ya bayyana cewa an tsinci gawarsa a ɗakin otel ɗinsa a ranar Alhamis da ta gabata.

A cewarsa, “Kwamandan Ogbonna mutum ne mai tsananin jajircewa a aiki. An shirya fita aikin haɗin gwiwa tare da shi da misalin ƙarfe 10 na safiyar Alhamis, amma hakan bai samu ba. An kira wayoyinsa akai-akai babu amsa, har lokaci ya ƙure bai bayyana ba.”

Takari: Rayuwar baƙin haure ’yan Najeriya mazauna Saudiyya Wata mata ta ƙone fuskar ’yar mijinta da tafasasshen man girki a Borno

Babafemi ya ƙara da cewa, “Duk da ƙoƙarin da ma’aikatan otel ɗin suka yi na buɗe ƙofar ɗakinsa, daga ƙarshe sai da aka yi amfani da makulli na musamman kafin a tarar da shi kwance ba shi da rai.”

Ya ce hukumar ta sanar da rundunar ’yan sanda ta jihar Kuros Riba nan take, inda kwamishinan ’yan sanda ya kai ziyara da kansa zuwa otel ɗin.

Yanzu haka bincike na ci gaba a kan asalin sanadin mutuwar kwamandan.

Shugaban hukumar NDLEA na ƙasa, Birgediya Janar Buba Marwa (mai ritaya), ya bayar da umarni ga kwamandan shiyyar 14 na hukumar, ACGN Mathew Ewah, da ya gaggauta komawa Kuros Riba domin ɗaukar ragamar shugabancin hukumar a jihar, har sai an kammala binciken da kuma gano musabbabin mutuwar babban jami’in.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gawar Kwamandan

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali

Daga Usman Mohammed Zaria

 

Majalisar Ƙaramar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa ta bayar da tallafin abinci ga fursunonin cibiyar gyaran hali ta Babura a matsayin wani ɓangare na ayyukan jin ƙai na majalisar.

Yayin ziyarar, Alhaji Hamisu Muhammad Garu ya bayyana cewa, wannan taimako ya biyo bayan lura da bukatun fursunonin yayin da ya kai ziyara ta duba cibiyar a baya.

A cewarsa, manufar bayar da tallafin ita ce don tallafa musu wajen kyautata rayuwarsu da kuma karfafa musu gwiwa su zama mutane nagari bayan sun fito daga gidan gyaran hali.

A nasa jawabin, jami’in da ke kula da cibiyar gyaran hali ta Babura, ASP Muhammad Ali, ya gode wa shugaban ƙaramar hukumar bisa wannan karamci, yana mai cewa taimakon ya zo ne a lokacin da ake matuƙar buƙata.

A yayin hudubarsa ga fursunonin, Babban Limamin Babura, Imam Salisu Aliyu, ya shawarce su da su nemi gafarar Allah, su kuma kara kusanci gare Shi, tare da rungumar canji mai kyau.

Kayan tallafin da aka bayar sun haɗa da buhunan masara, gero, shinkafa, garin rogo, man gyada, sinadaran dandano, gidan sauro da maganin kwari.

Manyan baƙin da suka raka shugaban ƙaramar hukumar a lokacin ziyarar sun haɗa da Hakimin Babura, Sarkin Bai Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha, jami’in ‘yan sanda mai kula da yankin, CSP Abdu Jinjiri, da jami’in Hukumar Tsaro ta Civil Defence, CSC Sunusi Usman Chamo, da sauransu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yayi Maraba Da Kalaman Da Hukumar IAEA Ta yi Kan Shirin Nukuliyarta
  • Uba Sani Ya Kaddamar Da Gidaje 100 Ga Waɗanda Rikici Ya Shafa A Jihar
  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci