Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-20@13:37:11 GMT

An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwa A Gundumar Bakori

Published: 20th, September 2025 GMT

An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwa A Gundumar Bakori

Gundumar Bakori ta jihar Katsina ta kaddamar da shirin dashen itatuwa domin rage zaizayar kasa a yankin.

A cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin aikin gona, Cigarin Bakori Alhaji Shehu Ishiye ya fitar, ya bayyana cewa Hakimin Bakori, Makaman Katsina Alhaji Garba Tukur Idris, ya yi kira ga jama’a da su daina sare itatuwa ba bisa ka’ida ba don kare muhalli.

Ya jaddada bukatar wayar da kai kan muhimmancin dasa itatuwa wajen habaka tattalin arziki.

Alhaji Garba Tukur Idris ya ce gundumar za ta tabbatar da cewa an kula da itatuwan da aka dasa yadda ya kamata domin cimma burin kare muhalli.

Hakimin ya bayyana cewa taron ya kuma kunshi rabon kayan abinci da tabarmi ga wadanda hare-haren ‘yan bindiga suka shafa a gundumar.

Alhaji Garba Tukur Idris ya sake tabbatar da kudirin masu rike da sarautun gargajiya na gundumar wajen tallafawa marasa galihu a cikin al’umma, tare da samar da muhalli mai kyau domin ingantacciyar rayuwa.

 

Suleiman Sani Rigachikun

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Dashen Itatuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jigawa Na Gabatar Taro A Abuja Domin Tattara Bayanin Kasafin Kudin 2026
  • Matasa 8 Sun Sami Tallafin Kasuwanci Na Miliyan 2 A Jigawa
  • An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
  • Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
  • Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya
  • Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Karin Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa