Aminiya:
2025-11-04@16:00:09 GMT

Yadda za ka dawo da kuɗinka da ka yi kuskuren turawa wa wani

Published: 20th, September 2025 GMT

Kimiyyar sadarwa ta kawo sauƙin rayuwa a harkokin kasuwanci da mu’amalar kuɗi ta banki. Yawaitar amfani da wayar hannu wajen yin hada-hadar banki a Nijeriya ya sa mutane da dama ke tura kuɗi cikin sauƙi.

A shekarar 2024 kaɗai, rahoton Hukumar Biyan Hada-hadar Banki ta Ƙasa (NIBSS) ya nuna cewa darajar kudin da aka tura ta hanyar waya ta kai Naira tiriliyan 41.

5, lamarin da ya nuna ƙaruwar kaso 74 cikin 100 daga shekarar da ta gabata.

Sai dai kuma hakan na iya kawo matsala, musamman idan aka yi kuskure aika kuɗi zuwa wani asusu daban. Wannan na faruwa sosai, musamman idan aka rubuta lambar asusu ko sunan mai asusu ba daidai ba.

Shin me ya kamata mutum ya fara yi idan ya yi kuskuren aika kuɗi zuwa wani asusu daban?

Takari: Rayuwar baƙin haure ’yan Najeriya mazauna Saudiyya Laifukan kisan ƙare dangin da Isara’ila ta yi a Gaza — Rahoton MƊD

Abu na farko shi ne gaggauta sanar da bankinka sannan ka kai rahoto ga bankin wanda ya samu kudin.

Dole ne ka rubuta ƙorafi a hukumance, ka bayar da cikakken bayanin mu’amalar, sannan ka haɗa da shaidu kamar rasir, bank statement, ko sakon alat na fitar kuɗin. Wannan zai tabbatar wa bankin cewa ba ka shirya aika kuɗin ba, kuskure ne kawai.

Da zarar banki ya samu rahoton irin wannan kuskure abin da zai fara yi shi ne sanya ‘PND’ a kan asusun wanda ya samu kuɗin. Wannan na nufin ba zai iya cire kuɗi ta yadda abin da zai rage bai kai abin aka yi kuskuren tura masa ba, har sai an kammala bincike.

Idan wanda ya samu kuɗin ya amince da cewa kuɗin ba nasa ba ne, banki zai mayar da kuɗin kai tsaye. Amma idan ya ƙi amincewa, banki ba zai iya ƙwace kudin ba sai da umarnin kotu.

Wani hanzari ba gudu ba, yana da kyau a sani cewa dokokin kare sirri sun haramta wa banki ya bayar da bayanan tuntuɓa na mai asusun kamar lambar waya ko adireshin email.

Banki kawai zai iya tuntuɓar sa domin tabbatar da gaskiyar rahoton da aka kai. Don haka, ka bi matakan doka maimakon bin ta bayan fage.

Idan mai asusun da ya samu kuɗin bai yarda a dawo da su ba, me za a yi?

Idan haka ta faru, dole sai ka nemi lauya wanda zai taimaka maka ka shigar da ƙara a kotu. Lauyan zai rubuta ‘application’ tare da affidavit (rantsuwar gaskiya) da ke dauke da cikakken bayani da shaidu – rasit, takardar bayanan kuɗi a banki da kuma takardar ƙorafin da ka rubuta wa banki.

Kotu za ta duba shaidar da ka gabatar sannan ta yanke hukunci ko za a dawo da kudin.

Shin wace kotu ake kai irin wannan kara?

Ya danganta da inda aka yi mu’amalar da kuma adadin kuɗin da aka tura.

Idan a Legas ne, idan kuɗin bai kai Naira miliyan 10 ba, ana iya kai ƙara a kotun Magistrate. Idan ya fi haka kuma, sai a Babba Kotu (wato High Court).

A Abuja kuma, idan kuɗin bai kai Naira miliyan 5 ba, ana iya kai ƙara a kotun yanki. Idan ya fi kuma, sai a ‘High Court.’

A dukkan wuraren, idan mutum ya so, zai iya shigar da ƙara kai tsaye a High Court, musamman idan kuɗin na da yawa.

Me mutum zai nuna a matsayin shaida kafin kotu ta amince da mayar da kudin? Amsa ita ce za ka nuna abubuwa masu muhimmanci guda hudu:

1. Shaidar cewa kuɗin ya fita daga asusunka (ta bank statement ko debit alat).

2. Bayani cewa ba ka da wata mu’amala ko yarjejeniya da wanda ya samu kuɗin.

3. Cikakken bayanin asusun wanda ya samu kuɗin (banki, suna, lambar asusu).

4. Hujja cewa ka kai rahoto ga banki kafin ka garzaya kotu.

Idan ba ka kawo waɗannan shaidun ba, kotu ba za ta bayar da umarnin dawo da kudin ba.

Shin me zai faru bayan kotu ta bayar da umarnin dawo da kuɗi?

Da zarar kotu ta yanke hukunci, dole ne ka kai takardar hukuncin ga bankin wanda ya samu kuɗin. Banki zai dauki matakin mayar da kudin cikin gaggawa. Idan bankin ya ƙi aiwatarwa, hakan za a ɗauke shi a matsayin saɓa wa umarnin kotu, wanda zai iya jawo wa bankin hukunci mai tsanani.

Sai dai kuma akwai abin da zai iya jawo tsaiko wajen dawo da kuɗin bayan umarnin kotun. Kamar idan ba a kai wa banki ko mai asusun da ya samu kuɗin umarni ko hukuncin kotu ba.

Idan ba a san adireshin wanda ya samu kuɗin ba, kotu na iya bayar da umarnin a isar da saƙon gare shi ta hanyar bankinsa.

Matakan kariya

Shawararmu ga mutane domin kauce wa irin wannan kuskuren ita ce:

1. A duba sau biyu kafin a aika kuɗi ta waya ko ATM.

2. A tabbatar da sunan mai asusu ya yi daidai da wanda ake son aika wa.

3. A kiyaye da saurin aika kuɗi ba tare da dubawa ba.

4. A adana shaidun mu’amala (saƙon alat, rasit, bayanin mau’amalar banki).

A takaice, idan mutum ya yi kuskuren aika kudi cikin wani asusu daban, kada ya yi shiru ko ya yi sakaci da lamarin.

Matakin farko shi ne gaggauta sanar da banki, sannan a nemi umarnin kotu idan wanda ya samu kuɗin ya ki mayar da su.

Duk da cewa tsarin yana ɗan wahala, shari’a na bayar da dama domin ƙwato haƙƙin mai asusun da ya yi kuskuren.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: takarda wanda ya samu kuɗin da ya samu kuɗin umarnin kotu

এছাড়াও পড়ুন:

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

 

Duk da cewa suna da karfi a fannin aikin soja, amma harinsu zai zama tamkar amfani da igwa ne wajen kashe sauro. Duk wani fifikon da suke da shi ba zai dore ba. Saboda haka, a zahiri wannan tambayar da wani mai amfani da yanar gizo ya yi, ta nuna rashin hankali cikin kalaman shugaban Amurka.

 

Sai dai kalaman sun dace da halayya, da salon musamman na shugaba Donald Trump. Wani lokaci, da gangan ya kan yi amfani da kalmomi, da aikace-aikace marasa ma’ana wajen samar da yanayi na rashin tabbas, ta yadda zai samu damar matsawa wani lamba, don tilasta masa ya yi wani aiki. Wannan dabara ce da wasu masanan kasar Amurka ke kira da “ka’idar mahaukaci”, watakila ta dace da halayyar shugaba Trump, abun da ya sa yake ta amfani da ita wajen kula da harkokin waje.

 

Kana wannan batu na yin barazanar kai hari ya dace da halayyar kasar Amurka. Kasa ce wadda ba ta mai da hankali a kan neman gano gaskiya ba, balle ma la’akari da bayanan da Nijeriya ta gabatar dangane da zargin da aka yi mata. Kai tsaye an yi fatali da ikon mulkin kai na Najeriya, da dokokin kasa da kasa, da ra’ayoyin kasashen yankin da ake ciki. A ganin kasar Amurka, tana iya tsoma baki a duk wani aiki, da aikata yadda ta ga dama, kuma idan za ta iya yin amfani da karfin tuwo wajen tilasta wani, to ba za ta taba tattaunawa da shi ba. Kawai kasar tana kokarin aiwatar da mulkin danniya ne a duniya.

 

Amma, a cewar wasu masana, “ka’idar mahaukaci” ba ko yaushe take yin tasiri ba. Saboda idan wani ya dade yana kwaikwayon mahaukaci, to, ba za a ci gaba da tsoronsa ba. Kana mulkin danniya na kasar Amurka shi ma ba zai dore ba, idan aka yi la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke tasowa cikin sauri a zamanin da muke ciki.

 

Ko ta yaya ya kamata Amurka ta daidaita kalamanta da ayyukanta? Kuma ta wace hanya ya kamata kasashe daban daban su yi mu’ammala da juna?

 

Na farko, ya kamata mu tabbatar da daidaito tsakanin mabambanta kasashe, da kuma bin dokokin kasa da kasa. Na biyu, ya kamata mu daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da neman daidaita harkoki ta hanyar yin shawarwari, maimakon tayar da rikici. Na uku, ya kamata mu dora muhimmanci kan jin dadin jama’a, ta yadda ba za a tsaya ga kula da mutanen gida kadai ba, wato a hada da al’ummun sauran kasashe. Ya kamata a lura da hakkinsu da bukatunsu. Wadannan abubuwa suna cikin shawarar da kasar Sin ta gabatar, dangane da inganta jagorancin duniya.

 

Watakila kasar Amurka ba ta yarda da wadannan ka’idoji ba tukuna, amma tabbas wata rana za ta amince da su. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani October 28, 2025 Ra'ayi Riga Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka? October 27, 2025 Ra'ayi Riga Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata October 23, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 
  • Kungiyar Hizbullah Ta yi Gargadin Mayar Da Martani Idan isra’ila Tayi Kokarin Kai Samame Ta Kasa
  • Sinner da Alcaraz za su buga wasan baje koli a Koriya ta Kudu
  • An kashe ’yan bindiga 19 yayin wani hari a Kano
  • Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 
  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci