Aminiya:
2025-11-04@21:17:09 GMT

Duk shugaban da bai yi aiki ba bai kamata a sake zaɓarsa ba — Jonathan

Published: 20th, September 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce duk wani shugaba da bai yi aiki yadda ya kamata ba, bai kamata a sake zaɓarsa ba.

Ya yi gargaɗin cewa maguɗin zaɓe na ɗaya daga cikin manyan barazana ga dimokuraɗiyya a Afirka, kuma idan ba a gyara tsarin ba, ’yan kama-karya za su zama wajen zama.

Yadda za ka dawo da kuɗinka da ka yi kuskuren turawa wa wani An tsinci gawar kwamandan hukumar NDLEA a otel a Kalaba

Jonathan, ya yi wannan jawabi ne a taron shekara-shekara na Tattaunawar Gidauniyar Goodluck Jonathan da aka gudanar a Birnin Accra, na Ƙasar Ghana.

Ya ce mutanen Afirka na son a yi amfani da ƙuri’unsu don su samu shugabanni da za su inganta ilimi, tsaro, kiwon lafiya, ayyukan yi.

A cewarsa, idan shugabanni suka gaza bayar da waɗannan abubuwa, jama’a kan rasa muradi da kyakkyawan fata.

Ya ƙara da cewa a inda ake gudanar da sahihin zaɓe, jama’a kan iya tsige shugaban da bai yi aiki , amma a ƙasashen Afirka, ’yan siyasa na amfani da maguɗin zaɓe don ci gaba da yin mulki ko da jama’a ba sa so.

Tsohon shugaban ya kuma yaba da yadda matasa ke ƙara shiga harkokin siyasa, sai dai ya jaddada cewa har yanzu suna buƙatar jagoranci da hikimar dattawa domin su yi nasara.

A wajen taron, Shugaban Ƙasar Ghana, John Dramani Mahama, tsohon Shugaban Ƙasar Najeriya Olusegun Obasanjo, da wasu shugabanni sun yi kira da a gaggauta gyara tsarin dimokuraɗiyya a Afirka.

Mahama ya ce dimokuraɗiyya ba za ta ɗore ba idan ‘yan Afirka ba su tsaya tsayin daka wajen kare ta da ɓunƙasa ta ba.

Ya ce dole a bunƙasa cibiyoyi, a kawo ci gaba, a tabbatar da gaskiya da riƙon amana, tare da kare ’yancin ’yan jarida.

Obasanjo, wanda shi ne ya jagoranci taron, ya ce yadda ake tafiyar da dimokuraɗiyya a Afirka a yanzu ba za ta ɗore ba, dole sai an yi wa tsarin gyara.

Sauran mahalarta taron kamar Shugaban Hukumar ECOWAS, Doktq Omar Touray, da Bishop Matthew Hassan Kukah na Katolika a Sakkwato, sun jaddada cewa dimokuraɗiyya a Afirka bai kamata ta tsaya kan zaɓe kawai ba, sai an haɗa da gaskiya da riƙon amana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dimokuraɗiyya gidauniya taro dimokuraɗiyya a Afirka

এছাড়াও পড়ুন:

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

 

Kwankwaso, wanda shi ne dan takarar shugaban kasa na NNPP a zaben 2023, ya fitar da wata sanarwa mai karfi yana gargadin cewa kalaman Trump na iya kara ruruta wutar rikicin addini da kuma kara ta’azzara rashin tsaro a kasar.

 

A shafinsa na X, tsohon gwamnan ya yi Allah-wadai da matakin Trump na ayyana Nijeriya a matsayin “kasar da ke da matukar damuwa,” wanda kuma ya yi zargin ikirarin “kisan kare dangi ga Kiristoci.”

 

Kwankwaso, ya yi kira ga Amurka da ta taimaka wa Nijeriya da tallafin fasaha da leƙen asiri maimakon barazana, sannan ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta zurfafa hulɗar diflomasiyya ta hanyar naɗa wakilai na musamman domin tattaunawa.

 

“Ga ‘yan uwana ‘yan ƙasa, wannan muhimmin lokaci ne da ya kamata mu jaddada haɗin kai maimakon rarrabuwar kawuna. Allah ya albarkaci Nijeriya,” in ji Kwankwaso.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi November 3, 2025 Manyan Labarai Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya November 2, 2025 Manyan Labarai Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar
  • 2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
  • Mataimakin Tsohon Shugaban Kasar Amurka Dick Cheney Ya Mutu A Yau Talata
  • Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Amurka Dick Cheney ya mutu
  • Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027
  • Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Tsagin Damagum da Anyanwu sun shirya mamaye hedikwatar PDP a yau
  • Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya