Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni
Published: 21st, September 2025 GMT
Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin, ta ce matsayin Sin dangane da batun kamfanin TikTok a bayyane yake, kuma tana jaddada aniyar gwamnatin kasar na martaba hakkokin kamfanoni yadda ya makata.
Ma’aikatar ta ce Sin na maraba da matakin gudanar da shawarwari da kamfanoni bisa doron dokokin kasuwa, ta yadda za a iya kaiwa ga shawo kan matsaloli daidai da dokokin kasar Sin, da ka’idoji, da daidaita moriyar dukkanin sassa masu takaddama.
Ma’aikatar ta ce Sin na fatan Amurka za ta dauki makamancin wannan tafarki, ta cika alkawuran da ta dauka, da samar da wata kafa ta adalci, marar nuna wariya, kuma ta bunkasa muhallin kasuwanci ga kamfanonin kasar Sin, ciki har da kamfanin TikTok, ta yadda zai ci gaba da gudanar da hada-hada a Amurka, da ingiza daidaito, da ci gaba mai inganci, da dorewar alakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU
Ya ƙara da cewa: “Mun cika dukkan buƙatunsu. Yanzu mun koma teburin tattaunawa, yanzu haka na zo wurin shugaba Tinubu ne don zayyana masa inda muka tsaya da ASUU.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA