Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Published: 19th, September 2025 GMT
Majalissar gudanarwar kasar Sin ta fitar da takardar bayani, game da bunkasa ci gaban mata mai taken “Nasarorin Sin a fannin bunkasa ci gaban mata a dukkanin fannoni a sabon zamani”.
Takardar bayanin da aka fitar a Juma’ar nan, na zuwa ne gabanin bude babban taron shugabanni na kasa da kasa na 2025, game da daidaiton jinsi, da karfafar rayuwar mata da zai gudana a nan birnin Beijing.
Takardar ta kunshi cikakkun bayanai na gabatar da falsafar kasar Sin, da ka’idoji da ayyukan kirkire-kirkire masu nasaba da ingiza daidaiton jinsi, da bunkasa rayuwar mata a dukkanin fannoni a sabon zamani.
Kazalika, ta fayyace muhimman nasarorin da matan kasar suka cimma, da tarin gudummawar da suka bayar, da jaddada himmar Sin wajen shiga a dama da ita a ayyukan hadin gwiwa na kasa da kasa masu nasaba da bunkasa rayuwar mata. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
Hukumar bunkasa ilimin gaba da sakandare ta jihar Jigawa ta shirya taron tattaunawa ga jami’an gudanar da shirin koyawa dalibai musamman wadanda suke da nakasu a jarrabawar NECO ko WAEC wato Remedial program don su sami nasarar cin jarrabawar da za ta basu damar ci gaba da karatu a makarantun gaba da sakandare.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban hukumar, Dr Abbas A Abbas ya bayyana cewar gwamnatin jihar jigawa karkashin jagorancin Malam Umar Namadi ta sahalewa hukumar gudanar da shirin da ta saba yi duk shekara wajen baiwa daliban da suka fadi a jarrabawar NECO ko WAEC koyarwa ta musamman.
Yana mai cewar, sahalewar na da nufin basu damar sake rubuta jarrabawar don su sami dukkanin abun da ake bukata da zai basu damar ci gaba da karatun gaba da sakandare.
Dr Abbas A Abbas yace wannan shirn daya ne daga irin shirye shiye guda 6 da hukumar ke gudanarwa wanda doka ta basu dama.
Ya kuma kara da cewar, makasudin wannan tattaunawar shine a zaburar da jami’an kan irin aikin dake gaban su na ilimantar da dalibai hanyoyin da za su bi wajen amsa tambayoyin da akeyi a jarrabawar NECO ko WAEC.
Yace hakance tasa hukumar ta gayyato kwararrun masana don su kara bayar da bita ga jami’an a fannonin jarrabawar da ta shafi turanci da lissafi da kuma irin kalubalen da dalibai kan fuskanta wajen amsa tambayoyin alokacin jarrabawa.
Dr Abass ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi wajen kokarin sa na bunkasa harkar ilimi wanda daya ne daga cikin kudure kuduren sa 12 na ciyar da jihar gaba.
A jawaban su daban daban, kwararriya mai baiwa Gwamna shawara a Basic Education, Dr Hauwa Mustapha Babura da mataimaki na musamman ga Gwamna a fannin ilimin manya, Alhaji Garba Makama Gwaram sun yabawa Gwamna Namadi bisa kokarin sa na tallafawa shirin da sauran shirye-shiryen da hukumar bunkasa ilimin manya ke gudanarwa don baiwa daliban da suka fadi a jarrabawa damar sanin makamar da za su sami damar sake yin wata jarrabawar.
Sun kuma yi kira ga Jami’an da zasu gudanar da shirin da su saka tsoron Allah da kishin taimakawa daliban don cimma nasarar da aka sa a gaba.
Kazalika, sun yabawa kokarin Baban sakataren gudanarwa na hukumar Dr Abbas A Abbas bisa jajircewar sa wajen habaka ilimin manya a fadin jihar Jigawa.
Radio Nigeria ya bamu rahoton cewar, a lokacin taron an gudanar da takardu daban-daban a kan sabbin dabarun da za’a bi don tallafawa daliban da basu damar sake rubuta jarrabawar musamman a fannin turanci da lissafi da kuma shawarwariin da za ayi amfani dssu don kwalliya ta biya kufin sabulu.
Fiye da jami’ai masu hiror da dalibai 131 ne da aka gayyata daga kananan hukumomi 26 suka halarci taron da aka gudanar a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake cikin sakatariyar jihar jigawa.
Usman Mohammed Zaria