An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
Published: 22nd, September 2025 GMT
Matsalar tsaro san rufe kasuwannin shanu a yankin Kwara ta Kudu da kuma ɗauke sansanin masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke Yikpata, Ƙaramar Hukumar Edu an mayar da ita zuwa Ilorin, hedikwatar jihar.
Ƙananan hukumomin biyu na Kwara ta Kudu da arewacin jihar na daga cikin wuraren da matsalolin tsaro suka fi taɓarɓarewa duk da ƙoƙarin gwamnati da hukumomin tsaro.
Sanarwar farko ta fito daga Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi bakwai na Kwara ta Kudu, inda suka bayar da umarnin rufe duk kasuwannin Kara a yankin.
Shugabannin —Abdulrasheed Yusuf (Ifelodun), Benjamin Jolayemi (Isin), Azeez Yakub (Irepodun), Awelewa Gabriel (Ekiti), James Fadipe (Oke-Ero), Sulyman Olatunji (Offa), da Akanbi Olarewaju (Oyun)— sun ce matakin ya zama dole don hana shigar ’yan ta’adda cikin kasuwanni.
Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyuSun bayyana cewa, ko da yake jami’an tsaro sun yi nasarar ragargazar wasu ƙungiyoyin ta’addanci, har yanzu ana gudanar da sauran rina a kaba, don haka rufe kasuwannin ya zama dole.
Sauran kasuwannin kayan amfanin gona kuma an taƙaita harkokinsu zuwa ƙarfe 6 na yamma.
Shugabannin sun amince cewa matakin na yin illa ga tattalin arziƙi, amma kare rayuka ya fi muhimmanci.
Sai dai wannan umarni ya haifar da suka daga masu ruwa da tsaki. Shugaban Miyetti Allah na jihar, Alhaji Shehu Garba, ya ce matakin bai yi nazari ba kuma bai ba ’yan kasuwar shanu dama su ba da shawara ba. Ya ce hakan zai durƙusar da harkokin kasuwanci, ya kuma ƙara tsananta halin ƙuncin tattalin arziki.
A sakamakon taron da sarakunan gargajiya suka kira a fadar Olupo na Ajase-Ipo, Oba Ismail Yahaya Alebiosu, shugabannin ƙananan hukumomi sun janye umarninsu.
An cimma matsaya cewa a buɗe kasuwannin dabbobi daga ƙarfe 6 na safe zuwa 6 na yamma a ranakun kasuwa. Haka kuma an yanke shawarar yin shawarwari da shugabannin kasuwar shanu don tabbatar da tsaro.
Sai dai wani mazaunin Ajase, Idrissu Musa, ya ce wannan matakin zai shafi harkokin kasuwannin shanu matuƙa, domin yawanci kasuwancin yakan fara ne daga ƙarfe 5 na yamma zuwa bayan ƙarfe 10 na dare.
Shi ma wani ɗan kasuwar shanu, Sulymane Mohammed, ya ce rufe kasuwa ba zai shafi ’yan bindiga ba, domin ba kasuwa suke bukata ba, amma dubban mutane da ke dogaro da ita ne za su shiga cikin matsala.
Matsar da sansanin NYSCA gefe guda kuma, hukumomin NYSC tare da amincewar gwamnati sun sanar da cewa, an ɗauke masu yi wa ƙasa hidima na NYSC dafa sansaninsu na dindindin da ke Yikpata, Ƙaramar Hukumar Edu, zuwa Kwalejin Kimiyya (Kwara Poly) da ke Ilorin saboda rashin tsaro.
Mazauna Lafiagi sun bayyana rashin jin daɗi da wannan matakin. Yinusa Michael ya ce, “Yankin ya kan bunƙasa tattalin arziki duk lokacin da ’yan bautar ƙasa suke nan. Suna kuma taimakawa wajen koyarwa a makarantunmu. Maimakon matsar da sansanin, gwamnati ta nemo mafita.”
Zanga-zanga da ƙalubaleRahotanni sun nuna cewa wannan ya biyo bayan taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Offa ƙarƙashin jagorancin Sanata Lola Ashiru, wanda ya jaddada muhimmancin tsara mallakar ƙasa domin rage rikice-rikice.
Bayan kwana kaɗan, matasa da shugabannin al’umma a Isin sun toshe hanyar Ilorin–Omu-Aran–Kabba domin nuna rashin jin daɗi kan yawaitar garkuwa da mutane. Sun yi zanga-zanga daga ƙarfe 8 na safe tare da rufe hanyar, abin da ya dakatar da zirga-zirga.
Wasu mazauna sun tsere daga ƙauyukan da abin ya shafa, inda wasu suka koma Ilorin ko hedikwatar ƙananan hukumomi domin samun kariya.
Matsayin gwamnati da jami’an tsaroKwamishinan ’yan sandan jihar, Adekimi Ojo, ya ce yanzu an daƙile ayyukan’yan bindiga, saɓanin da, inda ya gode wa Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da ya kawo batun ga mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu. Wannan ya kawo karin motocin sulke 16 da ƙarin sojoji a jihar.
Gwamna AbdulRazaq ya ce gwamnati na ƙoƙarin kawar da ’yan ta’adda a yankunan da abin ya shafa tare da haɗa kai da masu ruwa da tsaki.
Wani tsohon kakakin ’yan sanda a jihar, Ajayi Okasanmi, ya yi kira ga al’umma da su rungumi haɗin gwiwar tsaro.
Ya ce, “Ko wane makami ne, ba zai yi tasiri ba idan al’umma ba su bayar da haɗin kai ba. Ba za a sami zaman lafiya ba har sai kowa ya ɗauki tsaro a matsayin nauyim da ya rataya a kansa.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara
Sanarwar ta ƙara da cewa, an bayar da ƙarin kayayyakin da za a raba a matsayin tallafin ne daga Hukumar Kula da Ilimi ta Duniya (UBEC) da UNICEF.
A jawabinsa a wajen taron, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa gwamnatinsa ta zo ne da aikin ceto da sake gina jihar.
Ya ce: “Tun da farko mun gane cewa hanya mafi inganci wajen dawo da Zamfara kan turba ita ce saka hannun jari a zukatan al’ummarmu.
“A yau, a cikin wannan alƙawari, na yi farin cikin sanar da raba kayayyakin koyo da koyarwa 408,137 da gwamnatin jihar Zamfara ta sayo kai-tsaye.
“Wannan shi ne ɗaya daga cikin mafi girma na zuba jari a cikin albarkatun koyarwa da jiharmu ta taba gani. Ya nuna imanin mu cewa malamai ba za su iya yin nasara ba tare da kayan aikin da suka dace ba, kuma yara ba za su iya koyo ba tare da isassun kayan karatu ba.
“Amma wannan ƙoƙarin ba namu kaɗai ba ne, muna godiya tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya (UBEC), wadda ta samar da kayayyakin koyo da koyarwa 77,609 domin ƙara wa shirin gwamnatin jiharmu.
“Gudunmawar da suke bayarwa ta nuna cewa ana samun ci gaba mai kyau idan gwamnatoci a matakai daban-daban suka yi aiki tare, tare da haɗin kan jama’a.
“Muna gode wa abokan aikinmu na ci gaba, musamman UNICEF, da suka samar da littattafai masu muhimmanci 5,000. Waɗannan litattafan za su ba yaranmu ilimi mai muhimmanci na muhalli da kuma ilimin tattalin arziki, tare ba su ƙarin haske kan yadda duniya take da canjin yanayi.
“Kowanne daga cikin waɗannan kayan da jihar ta sayo, da gudunmawar UBEC, da tallafin UNICEF, na da ma’anarsa. Amma tare, sun ba da labari ɗaya mai ƙarfi, Zamfara ta zabi hanyar ilimi a matsayin ginshiƙin sake gina al’umma.”
Gwamna Lawal ya kuma yaba wa malaman Zamfara bisa sadaukarwar da suke yi a fannin ilimi.
“Dole ne na ɗauki lokaci don yaba wa malamanmu, babu wani abin da zai iya maye gurbin sadaukarwar malamin da ke zaburar da ɗalibai a kullum. Waɗannan albarkatun da muke rarrabawa za su kasance masu ma’ana ne kawai idan an yi amfani da su sosai ta hanyar masu sha’awar ilmantarwa.
“Ga iyaye, don Allah ku gane muhimmiyar rawar da ku ke takawa a ilimin yaranku. Littafi shi kaɗai ba ya isa ba tare da ƙarfafawa a gida ba. Ilimi yana farawa ne daga gida, tarbiyya da jagoranci ke kafa tushen nasara. Ina roƙon ku da ku bai wa makaranta muhimmanci, kula da ayyukan ilimi, kuma ku tunatar da yaranku cewa makomarsu ta dogara ne akan sadaukarwarsu wajen koyon karatu.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp