’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno
Published: 21st, September 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta kama mutum biyar da ake zargi da satar fakiti 7,871 na abincin yara, wanda aka fi sani da Tamuwa, wanda aka tanada don yara masu fama da cutar yunwa.
Kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar 19 ga Satumba, 2025 .
Ya bayyana cewa an gano kayan ne a samame guda biyu da aka kai a Maiduguri.
Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York An sanya tukwicin N10m domin kama makasan limamin coci a EnuguSamamen farko ya auku ne a ranar 12 ga Afrilu, lokacin da aka tsayar da wata mota a Njimtilo, kusa da Maiduguri, inda aka gano fakiti 3,314 na Tamuwa, wanda hakan ya sa aka kama mutum biyu.
Haka kuma, a ranar 9 ga watan Yuni, jami’an tsaro sun tsayar da wata mota a Legacy Estate, Maiduguri, inda aka gano ƙarin fakiti 4,557.
Wannan ya kai ga kama wasu mutum uku da ake zargi.
ASP Daso ya ce: “’Yan sanda ba za su lamunci karkatar da kayayyakin agaji ba, domin an tanade su ne don ceton rayuka, musamman na marasa galihu.”
An miƙa kayan da aka ƙwato ga gwamnatin Jihar Borno, ta hannun Kwamishinan Lafiya, Farfesa Baba Mallum Gana, domin raba su yadda ya dace.
A halin yanzu, an gurfanar da mutane biyar da aka kama a gaban kotu domin fuskantar hukunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda tamowa yara
এছাড়াও পড়ুন:
Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
Jami’i a Asusun yara na MDD y ace; Daga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu Yahudawa ‘yan share wuri zauna da sojojin HKI sun kashe kananan yaran Falasinawa 47,tare da yin gargadi akan hatsari dake tattare da hakan.
Manaja mai kula da yanayi na musamman a karkashin Asusun kananan yaran da MDD Recardo Peres ya ce; “Yan share wuri zauna da sojojin HKI sun kashe Kananan yaran Falasdinawa 47 a yammacin kogin Jordan da birnin Kudus tun daga watan Oktoba na 2023.
Haka nan kuma ya ce; Bayan abinda ya faru na barnar yakin tsawon shekaru biyu a Gaza, da tsagaita wutar da ake ketawa da kuma kashe yara a cikin sa’o’i kadan da su ka gabata, bai kamata a bar yammacin Kogin Jordan ya zama wani wajen tayar da hargitsi ba.
Haka nan kuma ya ce; Abinda yake faruwa a yammacin Kogin Jordan yana da hatsari sosai, domin yara suna mutuwa tun farkon fara yaki, don haka ya zama wajibi a kawo karshen hakan da gaggawa.
YAmmacin kogin Jordan dai yana fuskantar tashe-tashen hankula saboda hare-haren sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Da Kuma yahudawa ‘yan share wuri zauna.
A wani labarin daga Gaza, babban Darakta na Ofishin Yada Labarai na Gwamnati Dr. Ismail al-Thawabta, ya yi gargadin game da wani bala’i na jin kai da ke tafe yayin da hunturu ke gabatowa, ganin yadda Isra’ila ke ci gaba da hana shigar da tanti, da iskar gas zuwa yankin Gaza, duk da yawan lalata gidaje da matsugunan fararen hula.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan November 7, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci