A kwanan nan ne aka rufe taron kolin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai ko SCO a takaice, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin, inda shugaban kasar, Xi Jinping ya gabatar da shawarar tsarin inganta jagorancin duniya. Wakiliyar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, ta zanta da shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian, wanda ya halarci taron, inda ya ce, ana amfani da ma’aunai biyu a halin yanzu a duk duniya.

A cikin shawarar tsarin inganta jagorancin duniya da shugaba Xi Jinping ya gabatar, akwai wani muhimmin bangare na gudanar da harkokin duniya bisa dokokin kasa da kasa, wato ya kamata a mutunta ka’idoji.

Masoud Pezeshkian, ya ce bai kamata a aiwatar da ma’aunai biyu a fannin dokokin kasa da kasa ba, wato duk wata kasa, mai fama da talauci ko mai hannu da shuni, mai tasowa ko mai karfin tattalin arziki, babba ko karama, ya kamata a mutunta ta cikin adalci. Amma har yanzu ba a kai ga cimma wannan buri ba.

A ganinsa, ya dace sassan kasa da kasa su girmama wannan ka’ida, ta yadda za a iya aiwatar da shawarar tsarin inganta jagorancin duniya. Ya ce a hakikanin gaskiya, idan ana son yin watsi da ra’ayin nuna bangaranci, ya kamata a bi tsarin da aka kafa, gami da yarjeniyoyin da aka daddale a wajen taron kolin kungiyar SCO na wannan karo, tare da aiwatar da su a zahirance. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

A shekarar 2025 a gundumar Qiemo dake jihar Xinjiang ta kasar Sin, wasu sabbin sassan dausayi da ake iya nomawa sun bayyana a cikin makeken yankin hamada. A ’yan shekarun nan, an gyara yankin rairayi zuwa gonaki, wadanda fadinsu ya zarce murabba’in kilomita 40 a gundumar Qiemo. A cikin sama da shekaru 10, an yi kokarin raya wasu sassan dausayi da ake iya nomawa a cikin yankin hamada dake jihar Xinjiang, inda fadin gonakin da ake noman hatsi ya karu zuwa murabba’in kilomita dubu 8 ko fiye, al’amarin da ya sa Xinjiang ta zama jihar da ta fi samun karuwar hatsi da ake nomawa a duk fadin kasar Sin. Wani babban manomi dake wurin, mai suna Liu Yong, ya ce “Mun cimma fata mai kima sama da zinari a wannan hamada”.

A bana ne ake cika shekaru 70 da kafa jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kai ta kasar Sin, inda ake yawan ganin irin wannan labari mai dadi a duk fadin jihar, kuma Xinjiang na kara janyo hankalin jama’a daga sassan kasa da kasa.

A shekara ta 2024, adadin baki ’yan kasashen waje da suka shiga jihar don yawon bude ido ya wuce miliyan 5, adadin da ya karu da kaso 46 bisa dari, idan aka kwatanta da na shekara ta 2023. Wadannan baki ’yan kasashen waje sun zama masu gani da ido game da ci gaban jihar Xinjiang. Daya daga cikin sanannun mutane a shafukan sada zumunta na intanet, Ba’amurke Danny Haiphong, ya ce “A wasu lokuta, abubuwan da muke gani a kafafen yada labaran yammacin duniya, ba sa bayyana abubuwa masu kyau. Amma muna jin dadin rayuwa a jihar Xinjiang dake da yanayi mai annashuwa.”

A halin yanzu, akwai zaman lafiya da kwanciyar hankali, da wadata da kyan muhalli a jihar Xinjiang, inda jama’a ke jin dadin rayuwa da aiki a wurin, al’amarin da ya shaida nasarorin muhimman manufofin da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ke aiwatarwa a jihar a sabon zamani. Kana, a karkashin wadannan manufofi, an samu manyan sauye-sauye, gami da dimbin nasarorin da ba a taba ganin irinsu ba a tarihin jihar, inda aka shiga wani muhimmin lokaci na samun babban ci gaba, da gagarumin sauyi, kana jama’a suna kara samun moriya. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?
  • Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco
  • Duk shugaban da bai yi aiki ba bai kamata a sake zaɓarsa ba — Jonathan
  • Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
  • An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
  • Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
  • Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista
  • Uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu Ta Yi Kira Ga Zaman Lafiya A Duniya