Sanarwar ta ƙara da cewa, an bayar da ƙarin kayayyakin da za a raba a matsayin tallafin ne daga Hukumar Kula da Ilimi ta Duniya (UBEC) da UNICEF.

 

A jawabinsa a wajen taron, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa gwamnatinsa ta zo ne da aikin ceto da sake gina jihar.

 

Ya ce: “Tun da farko mun gane cewa hanya mafi inganci wajen dawo da Zamfara kan turba ita ce saka hannun jari a zukatan al’ummarmu.

 

“A yau, a cikin wannan alƙawari, na yi farin cikin sanar da raba kayayyakin koyo da koyarwa 408,137 da gwamnatin jihar Zamfara ta sayo kai-tsaye.

 

“Wannan shi ne ɗaya daga cikin mafi girma na zuba jari a cikin albarkatun koyarwa da jiharmu ta taba gani. Ya nuna imanin mu cewa malamai ba za su iya yin nasara ba tare da kayan aikin da suka dace ba, kuma yara ba za su iya koyo ba tare da isassun kayan karatu ba.

 

“Amma wannan ƙoƙarin ba namu kaɗai ba ne, muna godiya tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya (UBEC), wadda ta samar da kayayyakin koyo da koyarwa 77,609 domin ƙara wa shirin gwamnatin jiharmu.

 

“Gudunmawar da suke bayarwa ta nuna cewa ana samun ci gaba mai kyau idan gwamnatoci a matakai daban-daban suka yi aiki tare, tare da haɗin kan jama’a.

 

“Muna gode wa abokan aikinmu na ci gaba, musamman UNICEF, da suka samar da littattafai masu muhimmanci 5,000. Waɗannan litattafan za su ba yaranmu ilimi mai muhimmanci na muhalli da kuma ilimin tattalin arziki, tare ba su ƙarin haske kan yadda duniya take da canjin yanayi.

 

“Kowanne daga cikin waɗannan kayan da jihar ta sayo, da gudunmawar UBEC, da tallafin UNICEF, na da ma’anarsa. Amma tare, sun ba da labari ɗaya mai ƙarfi, Zamfara ta zabi hanyar ilimi a matsayin ginshiƙin sake gina al’umma.”

 

Gwamna Lawal ya kuma yaba wa malaman Zamfara bisa sadaukarwar da suke yi a fannin ilimi.

 

“Dole ne na ɗauki lokaci don yaba wa malamanmu, babu wani abin da zai iya maye gurbin sadaukarwar malamin da ke zaburar da ɗalibai a kullum. Waɗannan albarkatun da muke rarrabawa za su kasance masu ma’ana ne kawai idan an yi amfani da su sosai ta hanyar masu sha’awar ilmantarwa.

 

“Ga iyaye, don Allah ku gane muhimmiyar rawar da ku ke takawa a ilimin yaranku. Littafi shi kaɗai ba ya isa ba tare da ƙarfafawa a gida ba. Ilimi yana farawa ne daga gida, tarbiyya da jagoranci ke kafa tushen nasara. Ina roƙon ku da ku bai wa makaranta muhimmanci, kula da ayyukan ilimi, kuma ku tunatar da yaranku cewa makomarsu ta dogara ne akan sadaukarwarsu wajen koyon karatu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

Sabo da irin mawuyacin halin da ake ciki ta fannin tsarin jagorancin duniya musamman a daidai wannan lokaci, ya sa shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin jagorancin duniya a kwanakin baya, shawarar da ta yi nuni da cewa, ya kamata a tsaya tsayin daka a kan kin yarda da daukar matakai na kashin kai, tare da kiyaye matsayin MDD, don ta taka rawar da ba wanda zai iya maye gurbinta a cikin tsarin jagorancin duniya. Lallai kasar Sin ta gabatar da shawarar, musamman don neman dakile ayyukan nuna fin karfi da ake fama da su a duniya, tare da samar da mafita ga kasa da kasa da suka shiga duhu.

A sati mai zuwa, za a gudanar da babbar muhawara da ma babban taron tabbatar da shirin samar da kasashe biyu a yayin babban zauren MDD, kafin haka, manyan kawayen Amurka irinsu Birtaniya da Faransa cewa suka yi za su amince da kafuwar kasar Palasdinu, lamarin da ya sake shaida cewa, babu wanda zai iya hana adalci. Lokacin da Amurka ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa, ba yarjejeniyar zaman lafiya kadai ta jefa cikin kwadon shara ba, har da matsayinta na jagorancin duniya.

Tabbas “komai nisan dare gare zai waye”, duk duhun da Gaza ke ciki, haske zai bayyana. Fatan kasa da kasa na wanzar da zaman lafiya zai kai ga kawar da dukkan abubuwan da ke tarnaki tare da shimfida dauwamammen zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, wanda hakan zai bude mana sabon babin tsarin jagorancin duniya.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe
  • Komai Nisan Dare Gari Zai Waye