Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance
Published: 23rd, September 2025 GMT
Faransa ta bi sahun Birtaniya, Australia da Canada da sauran ƙasashen duniya sama da 140 da suka amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ’yanci.
Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ne ya tabbatar da amincewar gwamnatinsa na kafa ƙasar Falasdinu a hukumance.
Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa ArewaMacron ya bayar da tabbacin ne a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York.
Mista Macron ya ce lokaci ya yi da ya kamata a kawo ƙarshen yaƙin Gaza tare da sakin sauran Isra’ilawa 48 da Hamas ke garkuwa da su.
Ya ce lokaci kaɗan ne ya rage wa duniya ta iya wanzar da zaman lafiya, don haka ya ce bai kamata a jira ba.
Mista Macron ya yi Allah-wadai da harin na ranar 7 ga watan Oktoba da Hamas ta kai wa Isra’ila.
Shugaban na Faransa ya ce yana son ganin an samar da zaman lafiya a yankin ta hanyar samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kai da ke zama makwabtan juna.
“Babu wata hujja na ci gaba da yaƙin Gaza”, in ji Macron, yana mai ƙarawa da cewa “ya kamata a kawo ƙarshen komai.”
A yau ne dai tawagar jami’an diflomasiyyan Falasɗinu ta gudanar da bikin ɗaga tutar ƙasar a birnin Landan, kwana guda bayan da Birtaniya ta amince da Falasɗinu a matsayin kasa mai cin gashin kanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faransa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa tattalin arzikin kasar Iran nan gaba zai ginu ne bisa shirin bayan karewar man fetur ne, inda fasahohi da ilmi da kirkire-kirkire da kuma darussan da za’a dauko daga kasashe kawayen kasar a kungiyoyin BRICS da kuma SCO ne zasu zama abin dogaru.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto shugaban yana fadar haka ne a daren jiya Asabar a wani taro wanda yake magana a kan hanyoyin da Iran zata bi don bunkasa fasaha da ilmin kere-keren kasar da samar da ci gaba masu dorewa a kasar. Pezeshkiya yace sauye-suyen da sauri da ake samu a duniya musamman a yankin tekun fariya sun sanya dabarbarun ci gaba na sauyawa da sauri ga kasar Iran.
Ya ce dole ne Iran ta maida hankali wajen samar da dukiya ta hanyar samar da kamfanoni wadanda suka gina ayyukansu kan bincike da ilmi. Mu dauko ilmomin jami’o’immu mu maida su a aikace a cikin kamfanonimmu.
Sanna ya kara da cewa dole ne mu dauki korewar da kasashe mambobi a kungiyoyin BRICS da SCO mu yi amfani da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka September 21, 2025 Hizbullah Ta Yi Gayyar Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah September 21, 2025 Hamas Ta Yi Bukaci A Hukunta HKI Akan Rusa Asibitoci September 21, 2025 IRGC: Duk Wani Sabon Kuskuren Abokan Gaba Zai Fuskanci Mayar Da Martani Mai Tsanani September 21, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Wata Mota A Kudancin Labanon September 21, 2025 Iran Za ta Iya Shawo Kan Duk Wani Takunkumi Da Aka Sanya Mata . September 21, 2025 Pakistan:Yarjejeniyar Tsaro Da Suka Kulla Da Saudiya Kamar Kawancen Tsaro Na Nato Ne. September 21, 2025 Matatar Mai Ta Dangote Ta Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai A Nijeriya September 21, 2025 Isara’ila Ta Kaddamar Da Shirin Iko Da Wasu Yankuna A Yammacin Kogin Jodan. September 21, 2025 Iran za ta katse hulda da IAEA idan aka maida mata takunkuman MDD September 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci