Bello, ta kuma bayar da umarnin ƙara tsaro a duk faɗin ƙasar na , musamman a tashoshin mota, hanyoyin ruwa a jihohin da ke bakin teku, da kuma filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa.

Samamen ya biyo bayan bayanan sirri daga masu ruwa da tsaki da abokan hulɗa, waɗanda suka sanar da hukumar cewa akwai mutane da ake shirin safararsu a filin jirgin Abuja.

Bayan kusan sa’o’i 6 da aka gudanar ana bincike, an kama mutane biyar da ake zargi, sannan an ceto mutane 24 da aka so yin safarar su.

Adekoye ya ce waɗanda aka ceto, masu shekaru tsakanin 15 zuwa 26 ne, kuma an ɗauko su daga jihohin Kano, Katsina, Oyo, Ondo da Ribas.

An shirya kai su Iraq, Sudan, Masar, Saudiyya, Bahrain da Afghanistan.

Wasu daga cikinsu ba su ma san inda ake son kai su ba.

Ɗaya daga cikin matasan ta ce an fada mata cewa za a kaita Turai domin ta yi aiki ta samu kuɗi a dalar Amurka, kuma iyayenta sun amince.

Wata kuma ta ce mahaifinta ne ya yaudare ta domin a yi tafiyar da ita,kuma ta rantse za ta kai shi ƙara.

Shugabar hukumar ta nuna musu bidiyon wasu ’yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen waje sakamakon irin wannan safara.

Ɗaya daga cikin matasan ta ce: “Na yi ƙoƙari na riƙe hawayena lokacin da na kalli bidiyon waɗanda ake azabtarwa. Idan haka ne ba zan je ba. Na fusata da mahaifina saboda ya yaudare ni.”

Bello ta yi Allah-wadai da masu safarar mutane da masu ɗaukar ma’aikata ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda ke yaudarar ’yan Nijeriya domin su yi amfani da su ta hanyoyi daban-daban.

Ta ce ta gamsu da sakamakon aikin domin an samu nasarar karya hanyar wata babbar ƙungiyar masu safarar mutane da ke tura mutane zuwa ƙasashe masu hatsari, musamman a Gabas ta Tsakiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Safarar Mutane Zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

 

Amfani da jami’an tsaro:

Abu na farko dai dole ne kungiyoyi su yi aiki tare da yansanda, NSCDC, da jami’an tsaro na sirri wajen tsara tsare-tsaren tsaro a ranar da za su buga wasa, domin kuwa Bahaushe na cewa, “tun za a, ake shiri ba sai an dawo ba”, hakazalika yana da mahimmanci a tura isassun masu aikin kwantar da tarzoma (ba yansanda kawai ba) don sa ido kan magoya baya, lura da wuraren shiga/fita, da kuma taimakawa wajen rage turmutsitsi yayin wasa.

 

Amfani da CCTV:

Yawancin filayen wasa na gasar NPFL ba su da isasshen tsarin kyamarar CCTV, a cikin filayensu cewar bincike, samar da kyamarori masu sa ido na iya rage tashin hankali a cikin filayen wasa domin idan an ga wani motsi da ba a yarda dashi ba sai akai dauki da wuri.

 

Shingaye:

A tabbatar da cewa akwai shingen tsaro tsakanin yan kallo da cikin filin wanda ke hana saurin shiga filin wasa, bincike ya nuna wasu filayen gasar NPFL ba su da wani shamaki tsakanin yan kallo da filin wasa, hakazalika akwai bukatar raba magoya bayan kungiyoyin dake buga wasa zuwa mabanbantan wuraren zama, wannan yana rage rikici kai tsaye.

 

Matakan Ladabtarwa Masu Tsauri:

Hukumar NPFL ta riga ta sanya takunkumi mai tsanani ga Kano Pillars bayan wani tashin hankali da aka yi a wasanta da 3SC inda akaci kungiyar tarar Naira miliyan 9 da rabi, rage maki da kwallaye, da kuma rufe filin wasansu na gida a yanzu.

 

Hukunta Laifuka:

Ya kamata a gano wadanda suka mamaye filin wasa ko suka kai hari ga yan wasa da jami’ai (ta hanyar CCTV) kuma a gurfanar da su a gaban kuliya, wannan zai rage rikici a cikin filayen wasa.

 

Wayar Da Kai:

Akwai bukatar ci gaba da ilmantar da magoya baya kan halaye masu kyau, hatsarin tashin hankali, da kuma girmama jami’an wasa, kungiyoyi da NPFL za su iya gudanar da bita na magoya baya, amfani da kafofin sada zumunta, da kuma amfani da kungiyoyin magoya baya.

 

Rahoton Wasanni:

Bayan kowace wasa da aka buga akwai bukatar a gabatar da cikakken rahoto akan yadda wasan ya gudana, ta hakanan Za’a iya gano wuraren da suke bukatar gyara domin gyarawa kafin buga wasan gaba, hakazalika za a iya gano wanda ya nuna halayen rashin da’a a wasan domin a hukunta shi.

 

Jawo Hankalin Matasa:

Yawancin abubuwan tashin hankali suna faruwa ne da saka hannun matasa, saboda a cikinsu ne ake samun magoya baya masu zuciya da saurin fusata, akwai bukatar a nuna masu wasan kwallo WASANE BA FADA BA, mahukunta su shiga makarantu, majalisun matasa, da shugabannin al’umma domin sanar dasu ilimin kwallon kafa don koyar da girmamawa, wasa mai kyau, da kuma nusar dasu illolin tashin hankali.

 

Inganta Tsarin Shiga Filin Wasa:

Ayi amfani da hanyoyin zamani musamman na dijital wajen bayar da tikitin shiga filayen wasa da kuma guje wa cunkoso, idan da hali ana iya saka bayanan duk wanda ya shiga filin wasa wanda zai sa idan wani ya aikata laifi zai yi saukin kamawa ga hukuma.

 

Sakon Neman Afuwa Ga Jama’a Da Jagoranci:

Shugabannin kungiyoyi (kamar Ahmed Musa na Pillars) ya kamata su ci gaba da yin kira ga jama’a game da illar tashin hankali, amma kuma suyi hakan ta hanyar da magoya baya zasu gamsu kuma su fahimci abinda ake bukatar su Sani, Musa ya riga ya nemi afuwa a bainar jama’a kuma ya yi alkawarin daukar mataki.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Nazari Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna? November 16, 2025 Wasanni Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca November 15, 2025 Wasanni Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi November 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
  • Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
  • Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
  • Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • MDD: Mutane 100,000 Ne Su Ka Fice Daga Birnin Al-Fasher Na Kasar Sudan
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
  • Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya