‘Yan Bindiga Ta Sace Kwamishinan Zaɓe A Neja, Tsohon Shugaban SUBEB, Da Wasu
Published: 30th, September 2025 GMT
A lokacin, sun yi wa motar ‘yansanda ruwan harsasai yayin da ɗaya daga cikin jami’an ya ji rauni, amma an garzaya da shi asibiti.
Ya ƙara da cewa daga baya ‘yan bindigar sun sake tare wata hanya a gaba, inda suka sace fasinjoji a motoci uku.
Abiodun, ya ce an tura ƙarin jami’an ‘yansanda tare da sauran jami’an tsaro da mafarauta don bin sahun ‘yan bindigar, da nufin ceto waɗanda aka sace da kuma cafke masu laifin.
A wani samame daban, Abiodun ya bayyana cewa rundunar ‘yansandan tare da mafarauta sun kai farmaki wani dajin da ake zargin maɓoyar masu garkuwa, a cikin dajin Kokolo da ke Ƙaramar Hukumar Magama.
A lokacin arangamar da aka yi da ‘yan bindigar, an kashe uku daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunuka.
An kuma ceto wani daga cikin waɗanda aka sace.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya buƙaci al’umma su ƙara kula da tsaro tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, yayin da ’yan bindiga suka fara kai hare-hare a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina.
Sarkin, ya yi wannan kira ne yayin ziyarar jaje da ya kai wa al’ummar Faruruwa da ke Ƙaramar Hukumar Shanono a Jihar Kano.
Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16 Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — MuftwangA baya-bayan nan ’yan bindiga sun kai hari yankunan, inda suka sace shanu tare da yin garkuwa da mutane.
Sarki Sanusi, ya ce yawan hare-haren da ake fuskanta a yankin ya nuna cewa ana buƙatar kula da goyon bayan sarakunan gargajiya, gwamnati da kuma ƙungiyoyin sa-kai.
“Tsawon watanni da suka gabata, hare-hare sun ƙaru a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina, inda ’yan bindiga ke zuwa su sace shanu, su kashe jama’a, su yi garkuwa da maza da mata,” in ji shi.
Ya ce ya kai ziyarar ne domin jajanta wa mazauna yankin da abin ya shafa, tare da tabbatar musu da goyon bayan gwamnati, da kuma ƙarfafa musu gwiwa su taka rawa wajen kare ƙauyukansu.
“Nauyinmu ne a matsayinmu na shugabanni mu zo mu ga mutanenmu, mu yi musu ta’aziyya, mu kuma tabbatar musu cewa gwamnati da jami’an tsaro suna yin iya bakin ƙoƙarinsu,” ya ce.
Sarkin ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta tura jami’an tsaro da kayan aiki don tsaron yankin.
“Gwamna ya sayi motocin aiki, ya samar da kayan aiki, kuma mutane na gani da idonsu yadda sojoji da ’yan sanda ke yawan sintiri a yankin.
“Muna kuma ƙarfafa musu gwiwa su yi amfani da ’yan sa-kai wajen kare ƙauyukansu,” a cewarsa.
Sarki Sanusi, ya kuma bukaci al’ummomin Katsina da ke maƙwabtaka da yankunan da su tabbatar cewa yarjejeniyar sulhu da suke yi da ’yan bindiga ba za ta zama silar kawowa Kano hari ba.
Ya yi addu’ar Allah Ya wanzae da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa, tare da alƙawarin ci gaba da aiki tare da gwamnatin jihar domin kare rayukan jama’a.
“Muna rokon Allah Ya dawo mana da zaman lafiya, kuma za mu ci gaba da yin iya bakin ƙoƙarinmu tare da gwamnati domin tabbatar da tsaro a wannan jiha,” in ji shi.