ASUU ta bayar da wa’adin tsunduma yajin aiki a faɗin Nijeriya
Published: 29th, September 2025 GMT
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU) ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin makonni biyu domin tsunduma yajin aiki muddin ta ci gaba da sakaci kan wasu buƙatu da take nema a biya.
A sanarwar gargaɗi da ASUUn ta fitar yau Litinin, ta ce daga jiya Lahadi, 28 ga watan Satumba, za ta bai wa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 domin ta karkata akala kan buƙatun da take nema, ko kuma ta tsunduma yajin aikin gargaɗi na makonni biyu, inda daga nan zai rikiɗe zuwa na sai baba ta gani.
Shugaban ASUU, Farfesa Chris Piwuna, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya sa wa hannu bayan taron majalisar zartarwar ASUU na ƙasa da aka gudanar a jami’ar Abuja a ranar Lahadi.
Ya ce ƙungiyar ta gaji da yadda Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da nuna halin ko in kula da harkar ilimi, musamman batutuwan da suka daɗe suna tattaunawa a kai
ASUU ta wassafa jerin buƙatunta da suka haɗa da bitar yarjejeniyar 2009 da samar da isassun kuɗaɗen farfaɗo da jami’o’i da biyan bashin albashin malamai da kuma samar da tsayayyen tsarin samun kuɗaɗen gudanarwa na jami’o’i.
“Ina sanar da cewa, idan bayan wa’adin kwana 14 gwamnatin tarayya ta kasa aiwatar da waɗannan buƙatu, ƙungiyar za ta fara da yajin gargaɗi na makonni biyu kafin ta shiga yajin aikin sai baba ta gani,” in ji sanarwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Kungiyar Malaman Jami o i Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya buƙaci al’umma su ƙara kula da tsaro tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, yayin da ’yan bindiga suka fara kai hare-hare a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina.
Sarkin, ya yi wannan kira ne yayin ziyarar jaje da ya kai wa al’ummar Faruruwa da ke Ƙaramar Hukumar Shanono a Jihar Kano.
Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16 Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — MuftwangA baya-bayan nan ’yan bindiga sun kai hari yankunan, inda suka sace shanu tare da yin garkuwa da mutane.
Sarki Sanusi, ya ce yawan hare-haren da ake fuskanta a yankin ya nuna cewa ana buƙatar kula da goyon bayan sarakunan gargajiya, gwamnati da kuma ƙungiyoyin sa-kai.
“Tsawon watanni da suka gabata, hare-hare sun ƙaru a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina, inda ’yan bindiga ke zuwa su sace shanu, su kashe jama’a, su yi garkuwa da maza da mata,” in ji shi.
Ya ce ya kai ziyarar ne domin jajanta wa mazauna yankin da abin ya shafa, tare da tabbatar musu da goyon bayan gwamnati, da kuma ƙarfafa musu gwiwa su taka rawa wajen kare ƙauyukansu.
“Nauyinmu ne a matsayinmu na shugabanni mu zo mu ga mutanenmu, mu yi musu ta’aziyya, mu kuma tabbatar musu cewa gwamnati da jami’an tsaro suna yin iya bakin ƙoƙarinsu,” ya ce.
Sarkin ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta tura jami’an tsaro da kayan aiki don tsaron yankin.
“Gwamna ya sayi motocin aiki, ya samar da kayan aiki, kuma mutane na gani da idonsu yadda sojoji da ’yan sanda ke yawan sintiri a yankin.
“Muna kuma ƙarfafa musu gwiwa su yi amfani da ’yan sa-kai wajen kare ƙauyukansu,” a cewarsa.
Sarki Sanusi, ya kuma bukaci al’ummomin Katsina da ke maƙwabtaka da yankunan da su tabbatar cewa yarjejeniyar sulhu da suke yi da ’yan bindiga ba za ta zama silar kawowa Kano hari ba.
Ya yi addu’ar Allah Ya wanzae da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa, tare da alƙawarin ci gaba da aiki tare da gwamnatin jihar domin kare rayukan jama’a.
“Muna rokon Allah Ya dawo mana da zaman lafiya, kuma za mu ci gaba da yin iya bakin ƙoƙarinmu tare da gwamnati domin tabbatar da tsaro a wannan jiha,” in ji shi.