Hukumar Tsare-Tsaren Biyan Fansho PTAD ta nesanta jami’anta daga laifin jinkirin biyan hakkokin tsofaffin ma’aikata masu ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Abuja, hukumar ta bayyana cewa Babban Bankin Najeriya (CBN) ne ke da alhakin kai tsaye wajen tura kudaden fansho zuwa asusun tsofaffin ’yan kasa.

PTAD ta roƙi afuwa kan jinkirin da aka samu, tana mai kira ga masu karban gansho da su jira shigowar kudi daga CBN, tana mai jaddada cewa an kammala dukkan shirye shirye da suka wajaba tun da farko.

Wasu daga cikin tsofaffin ma’aikatan FRCN da NTA Kaduna sun bayyana bacin ransu kan ci gaba da jinkirin biyan hakkokinsu, musamman ganin cewa tsofaffin sojoji sun riga sun karɓi nasu hakkokin tun watannin baya, abin da suka kira abin takaici.

Wadanda abin ya shafa sun kuma jaddada goyon bayansu ga zanga-zangar da aka shirya gudanarwa mako mai zuwa, idan Ma’aikatar Kudi ta Tarayya ta kasa shawo kan matsalar cikin gaggawa.

SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka baje kolin kayan laifin da ’yan sanda suka kama a Abuja

Kalli ya da Kwamishinan ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya, Ajao Saka Adewale, ya yi hole ababen hawa da sauran kayan laifi da rundunarsa ta kama a gaban ’yan jarida a ranar Juma’a.

Hotuna: Abubakar Sadiq Isah.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa
  • NAJERIYA A YAU: Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka
  • Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato
  • Kissoshin Rayuwa Imam Alhassan (a) 118
  • Kissoshin Rayuwa : Imam Al-Hassan (a)
  • Xi Ya Bukaci Matasa Da Su Ba Da Gudummawar Cimma Nasarar Zamanantar Da Kasa
  • Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje
  • Gaza : Kungiyar Euro-Med ta bukaci a binciki harin Isra’ila kan jirgin ruwan Freedom Flotilla
  • HOTUNA: Yadda aka baje kolin kayan laifin da ’yan sanda suka kama a Abuja