Hukumar Tsare-Tsaren Biyan Fansho PTAD ta nesanta jami’anta daga laifin jinkirin biyan hakkokin tsofaffin ma’aikata masu ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Abuja, hukumar ta bayyana cewa Babban Bankin Najeriya (CBN) ne ke da alhakin kai tsaye wajen tura kudaden fansho zuwa asusun tsofaffin ’yan kasa.

PTAD ta roƙi afuwa kan jinkirin da aka samu, tana mai kira ga masu karban gansho da su jira shigowar kudi daga CBN, tana mai jaddada cewa an kammala dukkan shirye shirye da suka wajaba tun da farko.

Wasu daga cikin tsofaffin ma’aikatan FRCN da NTA Kaduna sun bayyana bacin ransu kan ci gaba da jinkirin biyan hakkokinsu, musamman ganin cewa tsofaffin sojoji sun riga sun karɓi nasu hakkokin tun watannin baya, abin da suka kira abin takaici.

Wadanda abin ya shafa sun kuma jaddada goyon bayansu ga zanga-zangar da aka shirya gudanarwa mako mai zuwa, idan Ma’aikatar Kudi ta Tarayya ta kasa shawo kan matsalar cikin gaggawa.

SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025

Hukumar da ke shirya jarabawa kammala karatun sakandire a Afrika ta Yamma (WAEC), ta saki sakamakon jarabawar SSCE na shekarar 2025.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Litinin, 4 ga Agustan 2025, tana mai cewa dukkan ɗaliban da suka zauna jarabawar yanzu za su iya duba sakamakon nasu a shafinta na intanet.

Za a mayar da gidan yarin da ya haura shekara 100 zuwa gidan tarihi a Kano An sace jariri sabuwar haihuwa a asibitin Ekiti

“WAEC na farin cikin sanar da ɗalibai da suka rubuta jarabawar WASSCE a shekarar 2025 cewa an saki sakamakon a hukumance yau Litinin, 4 ga watan Agusta,” in ji sanarwar.

WAEC ta buƙaci ɗalibai da su shiga shafin duba sakamako na hukuma a (http://waecdirect.org) ko (http://waecdirect.org) domin duba sakamakon su ta amfani da bayanan jarabawa da lambobin tantance sakamako wato result checker pins.

A nasa bangaren, shugaban ofishin WAEC na Nijeriya, Amos Dangut, ya bayyana cewa an samu raguwar kashi 33.8 cikin ɗari na sakamako masu kyau idan aka kwatanta da na shekarar 2024.

Da yake zantawa da manema labarai a birnin Legas, Dangut ya ce kashi 72.12 cikin ɗari na ɗaliban da suka samu makin credit ko fiye aƙalla darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi — adadi ne da ya yi kasa da na bara da kusan kashi 34 cikin ɗari.

“A ƙididdigar da muka yi tsakanin sakamakon jarabawar 2024 da na 2025, mun lura cewa an samu raguwar kashi 33.8 cikin ɗari a yawan ɗaliban da suka samu makin credit ko fiye a aƙalla darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi,” in ji shi.

Aminiya ta rawaito cewa wannan dai na zuwa ne bayan ɗalibai da iyaye da su kansu makarantun sakandare a faɗin ƙasar sun shafe makonni suna dakon fitowar sakamakon jarabawar na bana.

Jimillar ɗalibai 1,973,253 daga makarantu 23,554 da aka amince da su ne suka zauna jarabawar bana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Umurci A Bada Kulawar Lafiya Kyauta Ga Tsofaffin Ma’aikata Masu Karamin Fansho
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
  • Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba
  • Dr Muhammad Tahir Da Aka Yi Wa Barazanar Kisa Ya Bayyana Abin Da Ya Gani Na Masifa A Gaza
  • Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
  • WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati
  • An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna