Hukumar Tsare-Tsaren Biyan Fansho PTAD ta nesanta jami’anta daga laifin jinkirin biyan hakkokin tsofaffin ma’aikata masu ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Abuja, hukumar ta bayyana cewa Babban Bankin Najeriya (CBN) ne ke da alhakin kai tsaye wajen tura kudaden fansho zuwa asusun tsofaffin ’yan kasa.

PTAD ta roƙi afuwa kan jinkirin da aka samu, tana mai kira ga masu karban gansho da su jira shigowar kudi daga CBN, tana mai jaddada cewa an kammala dukkan shirye shirye da suka wajaba tun da farko.

Wasu daga cikin tsofaffin ma’aikatan FRCN da NTA Kaduna sun bayyana bacin ransu kan ci gaba da jinkirin biyan hakkokinsu, musamman ganin cewa tsofaffin sojoji sun riga sun karɓi nasu hakkokin tun watannin baya, abin da suka kira abin takaici.

Wadanda abin ya shafa sun kuma jaddada goyon bayansu ga zanga-zangar da aka shirya gudanarwa mako mai zuwa, idan Ma’aikatar Kudi ta Tarayya ta kasa shawo kan matsalar cikin gaggawa.

SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Murdyk ya halarci wasan karshe na gasar cin kofin Uefa Conference League da Chelsea ta doke Real Betis a watan da ya gabata, amma kuma ba a cikin tawagar Chelsea ba, a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, FA ta ce “Za mu iya tabbatar da cewa an tuhumi Mykhailo Mudryk da laifin keta dokar hana kara kuzari, ta hanyar amfani da wani abu da aka haramta, wanda kuma ya sabawa doka ta 3 da 4 a kundin dokokin FA na hana kara kuzari.

 

Zuwa yanzu Chelsea ba ta ce komai ba dangane da tuhumar da akeyiwa Murdyk amma a watan Disamba ta ce, ta na fatan dan wasan nata yayi nasara duba da cewa “Mykhailo ya tabbatar da cewa bai taba yin amfani da haramtattun abubuwa da gangan ba” tace a cikin sanarwar, a karkashin dokokin FA, yan wasa sunada yancin bukatar ayi masu gwaji na biyu bayan an samu tabbacin amfani da kwayoyi masu kara kuzari a gwajin farko, amma idan gwajin na biyu ya zo daidai da na farko to za a yanke masu hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
  • Kar a kuskura a shiga cikin yaƙin Iran da Isra’ila — MDD
  • Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran