Pezeshkian : Hare-haren watan Yuni kan Iran cin amanar diflomasiyya ne
Published: 24th, September 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai a watan Yuni a kan kasar.
A lokacin da yake jawabi a taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 ya shaidawa mahalarta taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York a yau Larabar cewa, hare-haren wani babban rauni ne ga zaman lafiya a yankin.
Shugaban ya ce hare-haren, wadanda suka afkawa garuruwa, gidaje, da ababen more rayuwa na Iran, yayin da ake ci gaba da tattaunawar diflomasiyya, “babban cin amanar diflomasiyya da raunana kokarin da ake yi na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ne.”
Pezeshkian ya zargi Washington da Tel Aviv da ruguza tattaunawar da gangan da karfin soji.
Shugaban na Iran ya ce hare-haren sun kashe kwamandoji, mata, yara, masana kimiyya, da kuma masu fada aji na kasa, tare da lalata cibiyoyin da kasashen duniya ke sa ido.
A wani share na jawabinsa shugaban kasar ta Iran ya fadawa wakilan kasashen duniya cewa: “Kisan jami’an gwamnati, kai hare-hare kan ‘yan jarida, da kuma kashe mutane saboda iliminsu da kwarewarsu, babban take hakkin bil’adama ne da dokokin kasa da kasa.”
Ya kuma yi Allah wadai da “kisan kare dangi a Gaza”, barna da keta hurumin kasashen Lebanon, Siriya, Yemen da ake yi, da “yunwar da aka jefa mata da yara, ya kuma sake nanata cewa Iran ba ta neman mallakar makamin nukiliya kamar yadda jagororinta magabata suka bada fatawa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jami’an Tsaron Amruka Sun Kai Hari Ofishi Da Gidan John Bolton September 24, 2025 Larijani: Donald Trump Yana A Matsayin Makwafin Adolf Hitler September 24, 2025 Fiye Da Falasdinawa 900,000 Ne Su Ka Yi Hijira A Cikin Gaza September 24, 2025 Imam Khamenei: Hadin kan al’ummar Iran a yakin kwanaki 12 ya sanya makiya kunya September 24, 2025 Larijani: Iran na kare tsaron kasa da azama September 24, 2025 Jagora: Iran Ba Za Ta Taba Yin Watsi Da Inganta Sinadarin Uranium Ba September 24, 2025 Larijani: Iran Tana Nazarin Shawarwarin Turai Da Na Rasha Domin Kare Muradunta September 24, 2025 Araqchi; Iran Da Norway Sun Tattaunawa Batun kyakkyawar Alakar Da Ke Tsakaninsu September 24, 2025 Groosi: Masu Binciken Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Suna Hanyar Zuwa Iran September 24, 2025 Kasashen Afirka Uku Sun Sanar Da Ficewa Daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka Ta Duniya September 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya
Mataimakin ministan harkokin wajen Iran kan harkokin ƙasa da ƙasa da shari’a ya jaddada muhimmancin kara karfafa dangantakar da ke tsakanin Tehran da Riyadh, yana mai cewa ci gaban kyakkyawar alaƙa tsakanin Tehran da Riyadh ba wai kawai yana da amfani ga ɓangarorin biyu ba ne, har ma zai kara karfafa zaman lafiya a yankin da ma a duniya.
Kazem Gharibabadi ya yi wannan furuci ne bayan ziyarar da ya kai Saudiyya da nufin fadada haɗin gwiwa da haɗin kai tsakanin manyan ƙasashen biyu.
Mataimakin ministan harkokin wajen ya jaddada cewa Iran da Saudiyya, waɗanda ke da alaƙa ta tarihi suna da kyakkyawan matsayi don yin hidima ga al’ummarsu da kuma taka domin ci gaban zaman lafiya a yanking abas ta tsakiya.
Gharibabadi ya yi cikakken bayani game da ganawarsa da Mataimakin Ministan Harkokin Waje na Saudiyya, Abdulrahman al Rassi.
Ya ce tattaunawar ta mayar da hankali kan ƙarfafa haɗin gwiwa a mataki na yankin da kuma na ƙasa da ƙasa.
Jami’an sun kuma yi musayar ra’ayoyi kan ƙarfafa muhimmiyar rawar da Ƙungiyar Haɗin Kan Musulmi (OIC) ke takawa.
Gharibabadi ya ce ya jaddada bukatar da ke akwai ga OIC ta taka muhimmiyar rawa wajen magance muhimman batutuwa, ciki har da yin Allah wadai da laifukan mamayar da Isra’ila ta yi a Gaza da kuma cin zarafin da take yi a yankin, tare da fadada hadin gwiwa tsakanin kasashe mambobin kungiyar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba November 6, 2025 Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi November 5, 2025 Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba November 5, 2025 China ta yi alkawarin ci gaba da tallafawa Najeriya bayan barazanar Trump November 5, 2025 Imam Khamenei: Rikici Tsakanin Iran da Amurka na asasi ne November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci