Komawar Natasha majalisa ya nuna haɗin kai zai iya yaƙar rashin adalci — Atiku
Published: 24th, September 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yaba da buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan a Majalisar Dattawa, inda ya ce haɗin kai ya yi nasara a kan zalunci.
A ranar Talata ne Majalisar ta buɗe ofishinta, bayan rufe shi da aka yi tun daga 6 ga watan Maris, 2025, lokacin da aka dakatar da ita na tsawon watanni shida saboda zargin karya ƙa’idojin majalisar.
Ko da yake Kotun Tarayya ta yanke hukunci a ranar 4 ga watan Yuli cewa dakatarwar “ta yi tsauri kuma an yi ta ba bisa ƙa’ida ba.”
Da yake mayar da martani, Atiku ya ce sake buɗe ofishin ya nuna cewa ’yan Najeriya za su iya yaƙar zalunci idan suka yi tsaya tsayin daka tare.
“Abin farin ciki ne ganin an buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan. Duk da cewa al’ummar Kogi ta Tsakiya sun yi rashi na tsawon lokaci ba tare da wakilci ba, wannan gwagwarmaya ba ta tafi a banza ba.
“Ta tabbata cewa idan muka haɗa kai, za mu iya yaƙar zalunci,” in ji shi.
Atiku, ya danganta dakatar da Natasha a matsayin yi wa dimokuraɗiyya hawan ƙawara a ƙarƙashin Shugaba Bola Tinubu.
Ya yi misali da dakatar da Gwamnan Jihar Ribas, Simi Fubara, da wasu ’yan majalisa na jihar.
“Waɗannan abubuwa ba keɓantattu ba ne,” in ji shi.
“Suna nuna shirin gwamnatin Tinubu yayin da zaɓen 2027 ke ƙaratowa; shirin raunana dimokuraɗiyya da kuma danne muryar jama’a ta kowane hali.”
Atiku ya yi alƙawarin cewa za su ci gaba da yin tsayin daka tare da yaƙar rashin adalci.
“Za mu yi amfani da duk wata hanya ta doka da dimokuraɗiyya domin kare dimokuraɗiyyarmu, kare amanar jama’a, tare da kuɓutar da ƙasarmu daga mulkin kama-karya,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dakatarwa Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa, ta koma ofishinta da ke harabar majalisar bayan ƙarewar wa’adin dakatarwar watanni shida da aka yi mata.
A wani bidiyon komawarta ofis da ya karaɗe shafukan sada zumunta, ’yar majalisar ta zargi Shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio da ɗaukarta a matsayin baiwarsa.
Yarima Salman ya jagoranci jana’izar babban mai ba da fatawa na Saudiyya Kotu ta hana NUPENG rufe Matatar ƊangoteA cewarta, kamar yadda Akpabio ke matsayin sanata haka ita ma sanata ce.
Sanata Natasha ta ce duk da cewa an dakatar da ita ba bisa ƙa’ida ba, ta riƙa sauke nauyin al’ummar mazaɓarta na Kogi ta Tsakiya, saboda a cewarta ba ta son al’ummarta su ji kamar an yi watsi da su.
Tun da safiyar yau ce rahotanni suka bayyana cewa an buɗe ofishin sanatar da ke Suite 2.05 a cikin ginin Majalisar Dattawan.
Gabanin komawarta, ’yan sanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa magoya waɗanda suka raka ta zuwa Majalisar Dattawa daga Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.
Bayanai sun ce magoya bayan sun yi tattaki ne domin raka sanatar zuwa majalisar domin komawa bakin aikinta.
Ana iya tuna cewa mako gabanin komawarta ne Sanata Natasha ta rubuta wa Majalisar Dattawan wasiƙa, wadda ta bayyana a niyyarta ta dawowa aiki bayan dakatarwa na tsawon wata shida, amma majalisar ta ce ta ɗan jira tukuna.
A watan Fabrairu ne dai tankiya ta ɓarke a zauren Majalisar Dattawa tsakanin shugaban majalisar da Sanata Natasha, lamarin dai ya kai ga har Akpabio ya umarci ɗaya daga cikin masu yi wa sandan majalisar hidima da ya fitar da ita daga zauren majalisar, kuma daga bisani aka dakatar da ita na tsawon wata shida.
Wannan lamarin ya kai ga har Sanata Natasha ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta hukunta Majalisar Dattawan Najeriya game da dakatarwar da aka yi mata.