Aminiya:
2025-11-09@11:45:50 GMT

Komawar Natasha majalisa ya nuna haɗin kai zai iya yaƙar rashin adalci — Atiku

Published: 24th, September 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yaba da buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan a Majalisar Dattawa, inda ya ce haɗin kai ya yi nasara a kan zalunci.

A ranar Talata ne Majalisar ta buɗe ofishinta, bayan rufe shi da aka yi tun daga 6 ga watan Maris, 2025, lokacin da aka dakatar da ita na tsawon watanni shida saboda zargin karya ƙa’idojin majalisar.

Darajar Naira ta ƙaru bayan CBN ya rage kuɗin ruwa Mawaki Davido ya ba matarsa kyautar motar miliyan 240

Ko da yake Kotun Tarayya ta yanke hukunci a ranar 4 ga watan Yuli cewa dakatarwar “ta yi tsauri kuma an yi ta ba bisa ƙa’ida ba.”

Da yake mayar da martani, Atiku ya ce sake buɗe ofishin ya nuna cewa ’yan Najeriya za su iya yaƙar zalunci idan suka yi tsaya tsayin daka tare.

“Abin farin ciki ne ganin an buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan. Duk da cewa al’ummar Kogi ta Tsakiya sun yi rashi na tsawon lokaci ba tare da wakilci ba, wannan gwagwarmaya ba ta tafi a banza ba.

“Ta tabbata cewa idan muka haɗa kai, za mu iya yaƙar zalunci,” in ji shi.

Atiku, ya danganta dakatar da Natasha a matsayin yi wa dimokuraɗiyya hawan ƙawara a ƙarƙashin Shugaba Bola Tinubu.

Ya yi misali da dakatar da Gwamnan Jihar Ribas, Simi Fubara, da wasu ’yan majalisa na jihar.

“Waɗannan abubuwa ba keɓantattu ba ne,” in ji shi.

“Suna nuna shirin gwamnatin Tinubu yayin da zaɓen 2027 ke ƙaratowa; shirin raunana dimokuraɗiyya da kuma danne muryar jama’a ta kowane hali.”

Atiku ya yi alƙawarin cewa za su ci gaba da yin tsayin daka tare da yaƙar rashin adalci.

“Za mu yi amfani da duk wata hanya ta doka da dimokuraɗiyya domin kare dimokuraɗiyyarmu, kare amanar jama’a, tare da kuɓutar da ƙasarmu daga mulkin kama-karya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa Majalisar Dattawa

এছাড়াও পড়ুন:

 Kamfanonin Jiragen Sama Da Dama Na Amurka Sun Dakatar Da Jigilar Matafiya Saboda Rufe Ayyukan Gwamnati

Kafafen watsa labarun Amurka sun ce, kamfanon jiragen sama sun dakatar da zirga-zirga 1330 a jiya Asabar saboda ci gaba da rufe ayyukan gwamnatin tarayyar kasar dalilin rashin cimma matsaya akan kasafin kudi a Majalisun kasar.

Masu sanya idanu akan kai da komowar jiragen sama ne su ka dakatar da aiki saboda ba za su karbi albashi ba, idan su ka yi aiki alhali ayyukan gwamnati suna a rufe.

Hukumar filayen jiragen sama ta tarayyar Amurka ce ta sanar da cewa masu aikin kula da zirga-zirgar jiragen sama a hasumiyoyin dake cikin filayane jiragen sama 25 sun dakatar da aiki.

Daga cikin garuruwan da tsaikon aikin ya shafa da akwai Chicago, Sanfarancisco, New York, New Rock da kuma Atalanta.

Tashar talabijin din CNN ta ce, adadin tafiyar jiragen saman da aka dakatar ta kai 1900.

Ana hasashen cewa zuwa jibi Talata 14 ga watan nan na Zuwamba za a sami Karin raguwar kai da komowar jiragen saman daga kaso 6% zuwa 10%.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Wasu Kasashe Takwas Sun Bukaci Ganin An kama Benjamine Netanyahu November 9, 2025 WFP: Ana Fama Da Matsananciyar Yunwa A Gabashin DRC November 9, 2025 Iran da Pakistan sun habaka cinikayyar kan iyaka don karfafa kasuwanci da tsaro November 9, 2025 Tanzania: ‘Yan sanda sun kama wani babban jigon adawar siyasa November 9, 2025 Martanin Iran ya haddasa wa Isra’ila hasarar fiye da Dala Miliyan 200 November 9, 2025 Biden Ya Caccaki Trump Bisa Tuhumarsa Da Kawo Barna November 9, 2025 Masar da Rasha sun tattauna batutuwan tsagaita wuta a Gaza da kuma  Sudan November 9, 2025 Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya November 8, 2025 Iraki Na Samun Zaman Lafiya Kuma Tana Kokarin Kawo Karshen Zaman Sojojin Ketare A Kasar November 8, 2025 Turkiya Ta Fitar Da Sammacin Kama Natanyaho Da Wasu Jami’ian Isra’ila Kan Yakin Gaza November 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Kamfanonin Jiragen Sama Da Dama Na Amurka Sun Dakatar Da Jigilar Matafiya Saboda Rufe Ayyukan Gwamnati
  • Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC
  • Tarayyar Afirka Ta Yi Kiran Da A Girmama ‘Yancin Kai Na Najeriya Da Rashin Tsoma Baki A Harkokin Gidanta
  • Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Ajax ta kori kocinta John Heitinga