Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Babban Taro Kan Shawarar Samar Da Ci Gaban Duniya
Published: 24th, September 2025 GMT
Jiya Talata 23 ga wata ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya halarci babban taro kan shawarar samar da ci gaba ga duniya baki daya, tare da gabatar da jawabi a hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya dake birnin New York na kasar Amurka.
A gun taron da kasar Sin ta dauki nauyin shiryawa, firaminista Li ya ce, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shawarar raya duniya baki daya a wajen babban taron MDD a shekara ta 2021, shawarar da ta mayar da hankali kan muradun daukacin bil’adama.
Mahalarta taron daban-daban, sun goyi bayan manyan shawarwarin duniya guda hudu da shugaba Xi ya gabatar, gami da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, tare da nuna babban yabo ga dimbin nasarorin da aka samu don inganta hadin-gwiwa a fannin aiwatar da shawarar samar da ci gaban duniya, da maraba da sabbin matakan hadin-gwiwar sassan kasa da kasa da suka shafi fasahar kirkirarriyar basira ta AI da kasar Sin ta gabatar. Har wa yau, bangarori daban-daban sun nuna cewa, ra’ayi da matakan kasar Sin sun dace da manufofin kundin tsarin mulkin MDD, kuma ya kamata a aiwatar da ra’ayin cudanyar sassa daban-daban, da kyautata tsarin shugabancin duniya, da taimakawa samar da ci gaba dake nuna juriya ga bangarori daban-daban, da kiyaye muradun kasashe daban daban, musamman kasashe masu tasowa. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: samar da ci gaba
এছাড়াও পড়ুন:
UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima a ranar Laraba zai gabatar da jawabin Najeriya a taron Babban Zauren Majalisar Dinkin duniya (UNGA) karo na 80 da ke gudana a birnin New York na Amurka.
Zai yi jawabin ne a madadin Shugaban Kasa Bola Tinubu tsakanin karfe 3:00 na yamma zuwa 9:00 na dare agogon birnin New York.
Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar WakilaiKamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa ana sa ran Najeriya za ta bayyana sabbin kudurorinta na kasa (NDCs) da aka sabunta a karkashin yarjejeniyar Paris yayin wannan jawabi.
A baya, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya halarci zaman bude taron Majalisar Dinkin Duniya, inda Shugaban Amurka, Donald Trump, ya gabatar da jawabi na musamman, yana maraba da shugabannin duniya zuwa taron.
Da yake magana da NAN kan muhimmancin jawabin na Najeriya Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Sadarwa (Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), Stanley Nkwocha, ya ce ana sa ran sakon Najeriya ya karade duniya.
“Ko a fannin diflomasiyyar ilimi, al’adu, wasanni, tsaro, ko diflomasiyyar tattalin arziki, Shugaba Tinubu ya sauya yadda Najeriya ke mu’amala da al’ummar duniya.
“Ya gyara salon manufofin kasashen waje na Najeriya.
“Idan kana son auna karfin muryar Najeriya a matakin duniya, ka tuna da jawabin da ya gabatar a UNGA na shekarar 2024.
“Jawabi ne mai karfi da ya bukaci a yi sauye-sauye, ciki har da karin kujeru ga kasashen Afrika a Kwamitin Tsaro na MDD,” in ji Nkwocha.
(NAN)