Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa: Gaza na gaf da afkawa cikin babbar masifa saboda zaluncin ‘yan mamayar Isra’ila

A yayin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke ci gaba da killace Zirin Gaza sama da watanni biyu, abubuwan da ke faruwa a kowace rana, abubuwa ne da suke yadda bala’i ke shafar kowane gida, kowane titi, da kowane yaro, tare da cewa a kowace rana, ana kara gargadin cewa; Lokaci ya fara kurewa don ceton abin da za a iya cetowa.

Ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya sabunta gargadi game da bala’in da ke tafe saboda ci gaba da rufe mashigar yankin da kuma tsaurara matakan hana shigowa da madarar jarirai, da abinci mai gina jiki, da kuma taimakon jin kai.

Hakan ya wurga yara sama da 70,000 cikin fuskantar matsalar Rashin abinci mai gina jiki, yayin da wasu yaran Falasdinawa ‘yan kasa da shekaru biyar 3,500 ke fuskantar barazanar yunwa. Kimanin yara 290,000 ne ke gab da mutuwa, yayin da fiye da yara miliyan daya ke fama da rashin isasshen abinci a kullum rana. Ofishin ya bayyana wannan lamari a matsayin kisan kiyashi da aka yi a cikin abin kunya da kasashen duniya suka yi shiru, inda ya yi kira da a dauki matakin gaggawa don kawar da wannan killacewar tare da kin ba da damar shigar da kayan agajin jin kai domin ceto rayukan yara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza

Rahotonni sun bayyana cewa: Har yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila ta ki bari an gano kashi 88% na irin laifukan da ta aikata a yakin Gaza ba

Jaridar The Guardian ta Birtaniya ta bayyana cewa: Hukumomin mamayar Isra’ila sun boye kusan kashi 88% na binciken laifukan yaki ko cin zarafin da sojojin mamayar Isra’ila suka aikata a kan Falasdinawa a zirin Gaza ba, ba tare da gabatar da tuhumce-tuhumce ko cimma matsaya mai kyau ba tun farkon fara kai hare-haren wuce gona da iri kan Zirin Gaza a watan Oktoban shekara ta 2023.

Rahoton ya nakalto Action on Armed Violence yana cewa: gwamnatin mamayar Isra’ila na neman dauke hankalin duniya kan rashin hukunta ta ta hanyar gujewa daukar alhakin manyan laifukan da suka faru a Falasdinu, ciki har da kisan Falasdinawa 112 yayin da suke yin layi don neman garin abinci a watan Fabrairun shekara ta 2024, a hare-haren sama wanda ya kashe Falasdinawa 45 a sansanin Rafah a watan Mayu, da kuma kisan Falasdinawa 31 da sojojin mamayar Isra’ila suka kai a cikin watan Yuni, duk a kokarin da gwamnatin mamayar Isra’ila take yi na gujewa daukan alhakin kisan kiyashin kan Falasdinawa, duk da duniya ta tabbatar da hakan a watan Yuni.

Rahoton ya tattara kararraki 52 da hukumomin mamayar Isra’ila suka bayyana aniyarsu ta gudanar da bincike ko gudanar da bincike na hakika, wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa sama da 1,300 da kuma jikkata kusan 1,880. Sai dai yawancin waɗannan lamuran ba su haifar da tabbataccen sakamako ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tsohon Shugaban Amurka Joe Biden Ya Caccaki Trump Kan Rusa Kundin Tsarin Mulkin Kasar August 3, 2025 IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba August 3, 2025 Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza   August 2, 2025 Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
  • MDD ta yi gargadi  game da mummunar matsalar da yunwa ka iya haifarwa ga al’ummar Gaza
  • Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza
  • Shirin ACRESAL Zai Samar Da Injinan Ban Ruwa Masu Amfani Da Hasken Rana A Jigawa
  • Jamus ta soma jefa kayan agaji a Zirin Gaza
  • Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja
  • Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
  • Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka
  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF