Sojonin Yemen Ta Kakkabo Jiragen Yakin Amurka Wadanda Kimarsu Ya Dalar Amurka Miliyon $200 A Makonni 6
Published: 25th, April 2025 GMT
Sojojin kasar ayemen sun kakkabo jiragen yaki na kasar Amurka wadanda ake sarrafashi daga nesa a kan kasar Yemen, da dama wadanda kimarsu ya kai dalar Amurka miliyon $200 a cikin makonni 6 kacal.
Tashar talabijin ta Pressstv a nan Tehran ya bayyana cewa wadan nan jiragi suna aikin leken asiri ne a kan kasar ta Yemen, kuma duk da cewa suka tashi fiye da kafa 40,000 a sama, amma sojojin yemen suna iya kakkabosu.
Wannan yana zuwa ne a dai lokacinda shugaban kasar Amurka Donar Trump ya kara umurnin a kara yawan hare-haren da ake kaiwa kasar ta Yamen.
Mafi yawan hare-haren da suke kaiwa yana kasa mata da yara da kumalalata kamfanoni da kuma cibiyoyin samar da ruwa ko ajiyar makamashi ne .
Don haka hare-haren basa kaiwa ga makaman sojojin kasar Yemen wadanda suke karkashin kasa kuma nesa daga inda makaman Amurkka zasu samesu.
Amurka dai ta fara yake da Yemen ne don tallafawa HKI kan hare –haren sojojin yemen kanta tun baya sake dawoda yakin dofan al-aksa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta Zuwa Waje
Mai magana da yawun hukumar da take kula da filin saukar jiragen sama ta Ben Gorion ta sanar a yau Asabar cewa an rufe filin saukar jiragen saman har zuwa wani lokaci a nan gaba, bayan da aka dauke dukkanin jiragen sama zuwa kasashen Cyprus, Greece da kuma Amurka.
Mai Magana da yawun hukumar filin saukar jiragen saman na Ben Gorion Lisa Daiper ta bayyana ce; Babu wani lokaci takamaimai da aka tsayar domin sake bude filin saukar jiragen saman na Ben Gorion.”
A gefe daya jaridar “Maariv’ ta bayyana cewa; An dauke dukkanin jiragen sama zuwa filayen jiragen saman a kasashen turai.
Haka nan kuma ta kara da cewa; An dauki 14 daga cikin jiragen saman na HKI zuwa filin saukar jiragen saman a Laranka da Papus dake tsibirin Cyprus da su ne filayen jiragen sama na nahiyar turai mafi kusa da HKI.
Su kuwa jiragen da shugabannin ‘yan sahayoniya suke shiga an kai su ne zuwa filin jirgin sana na birnin Athenia na kasar Girka, wasu kuwa zuwa kasashen Bulgari da Faransa.
Dauke jiragen na ‘yan sahayoniya dai ya zo ne saboda tsoron kar makamai masu linzami na Iran su isa gare su.