Yunkurin Matasan Nijeriya Na Son Zama Attajirai A Dare Daya Ta Hanyar Caca
Published: 11th, April 2025 GMT
Kazalika, a wani binciken kwanan baya na gama gari kan yawan alummar kasar, ya gano cewa, kaso 53 na wasu matasan kasar, a kullum suna rungumar wannan dabi’ar.
Sai dai, muna sane da cewa, wasu ‘yan Nijeriya, na kallon yin cacar tamkar wata aba ce, ta nishadi kawai, amma wasu bincike sun bayyana cewa, wani dan bangere na mutanen da ke yin cacar ne kawai, ke samun a cacar, inda akasarin sauran, ke tabka asarar kudadensu da suka zuba a cikin cacar.
An dai jima ana yin caca a kasar, wadda a shekarun baya, ake yi mata wani kallon kan abinda bai dace ba, kamar dai yadda Coci ta alakanta ta, a matsayin hanyar yin arzikin dare daya
Idan za a iya tunawa, bangare na 22 na sashe 236 na kundin dokar aikata manyan laifuka na 1990, Gwamnatin Tarayya ta halasta wasu nau’uka na yin caca, musamman domin ta samar da kanta, kudaden shiga.
Dokar ta fayyace tsakanin wasan kwarewa wanda yake an halasta da kuma wani wasan, na neman sa a, wanda aka haramta.
Wasu nau’ukan na cacar da aka halasta, sun hada da, cacar da ake sayen wani Tikiti domin shiga gasar zamowa Zakara kan wani abu da aka sanya kamar mota ko wani gida da sauransu.
Amma abin takaici, hakan ya sanya cacar ta kara karbuwa ga wasu alummar gari, musamman a tsakanin yaran da suke da kanannan shekaru.
Kazalika, mun fi lura da akasarin nau’ukan cacar da ake yi a kasar, misali wacce a yanzu ake yi kasar kamar ta gasar ta Kwallon Kafa da sauransu, da ake yi, a kafar Internet.
An yi hasashen cewa, rashin aikin yi, sun arzirta a dare daya, matsain tattalin arziki, su ne, kusan hummulhaba’isin da ke sanya wasu mutanen kasar, musamman matasa ke rungumar wannan halin, inda kuma hakan, ke kara haddasa, aikata manyan laifuka.
Muna damu makuka kan yadda wannan halin, ke kara tarwatsa, tarbiyar wasu matasan kasar, da suka rungimi wannan dabi’ar.
A saboda haka, akwai bukatar Gwamnatin Tarayya, ta dauki matakin kan wannan batun.
Fanin cacar gasar wasa ta Nijeriya, ta kasance a kan gaba a Afirka, duba da yadda a kasuwar a 2023 aka samu ribar da kai ta akalla dala biliyan biyu,
Kazalika, duba da yadda a fannin ake samun sama da tiriliyan uku ko kuma sama da haka, cacar gasar wasa ta Nijeriya, sama da shekarun da suka wuce, wannan fannin, sai kara tumbatsa yake yi kasar, wanda haka na faruwa ne, saboda matsin tattalin arziki, karuwar matasa marasa aikin yi da kuma kara bunkasar yin amfani da wayoyin tafi da gidanka.
Ana dai kara ci gaba da samun irin wadannan shagunan da ake gudanar da irin wannan cacar ta gasar wasanni kusan ako wanne tituna da kuma a dandalin sada zumunta, wanda hakan, ya bai matasan kasar da damar, rungumar dabi’ar ta caca, musamman domin su samar wa kansu, da kudaden shiga,
Zamu iya cewa, mun jahilaci cewa, kasancewar yanayin matsalin tattalin arziki da Nijeriya ke fuskanta ne, ya hadda samun karin guraren da ake gudanar da gasar ta cacar wasanni.
A cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa NBS, samun karuwar matasa marasa aikin yi a kasar, ya sanya su daukar matakan da suke ganin ya dace da su, domin su samarwa da rayuwarsu mafita, musamman yadda suke kara rungumar cacar ta gasar wasanni, da suke mata kallon mataki na zuba hannun jari.
An kiyasata cewa, a wannan fannin, ana samaun akalla Naira tiriliyan uku a shekara, wanda kuma ake kara samun ‘yan kasuwa na tallata hajojinsu ta hanyar amfani da kafar sada zumunta, daukar nauyin tallace-tallacen, da suka samu amincewar wasu fitattu.
Wannan ya nuna yadda rahoton Mujallar Lancet ya bayyana matasan da suka rumgumi cacar ke shafe sa’oi 24 suna gudanar da cacar, wadda kuma ke shafar lafiyarsu da barnatar da kudaden da suke yi.
A bangaren mu, tsawon lokacin da ake ci gaba da fuskanta na kangin matsin tattalin arziki a kasar wanda hakan, ya tilatsa wasu matasan yin cacar ta wasanni, abin damuwa ne.
Bugu da kari, yadda wannan batun ke shafar tabin hankalin matasa da ke yin dabi’ar abin damuwa ne, musamman ganin yadda kwararru a fannin kiwon lafiyar ‘yan Adam suka yi gargadin cewar kara samun matasa masu yin dabi’ar a kasar, na kara jefa matasan a cikin matukar damuwa, inda har wasu matasan saboda fusatar rashin samun nasara a dabi’ar, suke kashe kansu ko kuma rungumar tu’ammali, da kayan maye.
Mai makon su rinka zuba kudaden su a halastattun sana’oi, amma sai buge za zuba kuaden, a cacsar gasar wasannin
Duk da ikirarin da irin wadannan kamfanonin na cacar gasar wanni ke yi cewa, suna samar da nishadi da damar samar da ayyukan yi ga matasan ne, ammu mu dai, mun yi ammanar cewa, suna dai kawai amshe ‘yan kudaden matasan ne.
Babu wata tamtama, akwai bukatar a kakabawa fannin da irin wadannan kamfaonin na cacar gasar wasannin, tsauraran matakai.
Kazalika, akwai matukar bukatar Hukumar sa ido kan irin caca ta kasa NLRC wacce kuma ke sa ido kan cacar gasar wasanni ta kara karfafa dokokin yin gasar cacar ta wasanni tare da daukar matakan da suka kamata, ciki har da sanya dokar tallace-tallace da iyakance yawan kudaden da ake zubawa a cikin cacar, kamar dai, yadda ake yi wasu kasashen duniya.
Hakazalika, ya zama wajibi, Gwamnatocin Jihohi su tashi tsaye, wajen samar da tsare-tsaren da matakai da za su hana matasa shiga cikin dabi’ar.
Idan har mahukunta a kasar ba su samar da daukin da ya dace ba, yunkurin matasan na son arzircewa a dare daya, za ta ci gaba da kasancewa, wanda hakan kuma, zai shafi makoyar matasan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arziki gasar wasanni wasu matasan cacar gasar
এছাড়াও পড়ুন:
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bugu da kari kuma, gudummawar da Nijeriya ke bayarwa ga kokarin wanzar da zaman lafiya a duniya ba za su misalta tu ba, wanda hakan ke jaddada aniyarta na inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. Manufofinta na kasashen waje a al’adance suna nufin ingantawa da kuma kare muradun Nijeriya tare da tallafa wa hadin kan Afirka.
Gabatar da ajandar “4D”, a sakamakon haka, yana wakiltar sauyin da aka samu a lokacin da ya dace, wanda hakan zai bude damar karfafa hadin gwiwar da kasashen duniya, tabbatar da zaman lafiya na duniya, da kuma bunkasa matsayin Nijeriya a idon duniya. Sai dai, nasarar wadannan manufofin ya ta’allaka ne a kan aiwatarwar su mai inganci.
Ya kamata a lura da cewa Nijeriya ta tsunduma cikin harkokin diflomasiyya da dama a bara, ciki har da kulla wasu muhimman yarjejeniyoyi da Jamhuriyar kasar Sin. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya ziyarci Abuja, domin jaddada alkawuran da aka dauka a yayin taron dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC) na shekarar 2024, inda aka rattaba hannu kan wasu muhimman yarjejeniyoyi guda 10. Hakazalika, firaministan Indiya Narendra Modi ya ziyarci Nijeriya, inda ya bayyana aniyar kasarsa na zuba hannun jari a wasu muhimman sassa kamar a bangaren noma, samar da abinci, sadarwa, fasaha da bayanai, da kuma tsaro.
Shugaba Tinubu ya kuma gudanar da rangadin diflomasiyya, inda ya halarci taron G20 a Brazil da kuma kai ziyara a Faransa da Afirka ta Kudu da dai sauransu. Wadannan alkawurra an yi su ne da nufin karfafa martabar Nijeriya a idon duniya da kuma samar da fa’idodi na gaske ga kasar.
Duk da yake wadannan tafiye-tafiye na diflomasiyya abin yabawa ne, amma kuma dole ne su kasance su samar wa da kasar jari mai ma’ana da fa’ida ga ‘yan Nijeriya.
Sai dai a halin yanzu, hakan ya yi nisa daga zahirin abin da yake faruwa. Dole ne gwamnatin Tinubu ta dauki matakai masu muhimmanci domin tabbatar da cewa manufofin kasashen waje na Nijeriya sun fifita muradun kasa tare da kare ‘yan kasarta a kasashen waje. Wannan shi ne ainihin manufar “4D”.
Za a iya danganta raguwar tasirin Nijeriya a fagen duniya da tabarbarewar tattalin arzikin da aka shafe tsawon shekaru ana yi, wanda ya tilastawa ‘yan kasar da dama neman ingantacciyar damammaki a kasashen waje, galibi a cikin yanayi mai wahala da wulakanci. Idan ana son a sauya wannan hali, dole ne gwamnatin Tinubu ta gaggauta farfado da tattalin arzikin kasar domin fitar da miliyoyin mutane daga kangin talauci.
Ana iya cimma wannan ta hanyar jawo hankalin masu zuba hannun jari daga kasashe irin su Indiya, Sin, Afirka ta Kudu, da Faransa, musamman a fannoni kamar hakar ma’adinai, aikin gona, da ICT, wadanda ke da fa’ida masu yawan gaske. Har ila yau, dole ne Nijeriya ta mayar da hankali wajen bunkasa harkokin kasuwanci na yanki, kamar samar da kasuwar samun kayayyakin amfanin gona da za su hada masu samarwa da masu shigo da kayayyaki, ta yadda za a rage dogaro da kuma fadada kasuwancin kayayyakin Nijeriya.
Domin manufofin Nijeriya na kasashen waje su yi tasiri, dole ne ta fara magance bukatun ‘yan kasarta. Gwamnatocin da suka gada sun yi ta fafutika wajen yin amfani da damar hadin gwiwar kasa da kasa domin samar da ayyukan yi, da jawo jari, da kawar da talauci. Alkaluman sun yi muni: a tsakanin 2023 zuwa 2024, kashi 63% na ‘yan Nijeriya – kimanin mutane miliyan 133.3 – suna rayuwa cikin kangin talauci, a cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS). Rashin aikin yi na matasa ya kasance wani muhimmin batu, a yayin da hauhawar farashin kayayyaki ya kai kashi 34.6% a karshen shekarar 2024, inda hauhawar farashin kayayyakin abinci ma ya fi kamari.
Rahoton Tattalin Arziki na Afirka (ERA 2023) ya jaddada gaggawar magance kalubalen tattalin arzikin Nijeriya. Ya gano manyan gibi guda uku – kwarewa, abubuwan more rayuwa, da kuma ingancin cibiyoyin (gudanarwa) – wadanda dole ne a gyara su domin gina tubuli mai karfi domin ci gaba.
Mun yi imani wannan ita ce hanya madaidaiciya. Dole ne gwamnatin Tinubu ta fito da tsare-tsare masu kyau na ci gaban kasa, samar da shugabanci nagari, da aiwatar da gyare-gyaren tsari a dukkan bangarori masu muhimmanci.
A yayin da Nijeriya ke fuskantar tabarbarewar tattalin arziki da kuma yanayi na cire fata a tsakanin ‘yan kasar, dole ne gwamnatin Tinubu ta tashi tsaye tare da rungumar tsarin hulda da kasashen waje na Ambasada Yusuf Tuggar. Manufofin kasashen waje da zai jawo zuba hannun jari, samar da ayyukan yi, da magance tushen talauci, tabbas wadannan a karshe za su samar da nasara. Da duk wani abu da ka iya rage barazana ga barin Nijeriya ta makale a tsaka mai wuya a tsakanin yiwuwarsa da tabarbarewar ta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp