Yunkurin Matasan Nijeriya Na Son Zama Attajirai A Dare Daya Ta Hanyar Caca
Published: 11th, April 2025 GMT
Kazalika, a wani binciken kwanan baya na gama gari kan yawan alummar kasar, ya gano cewa, kaso 53 na wasu matasan kasar, a kullum suna rungumar wannan dabi’ar.
Sai dai, muna sane da cewa, wasu ‘yan Nijeriya, na kallon yin cacar tamkar wata aba ce, ta nishadi kawai, amma wasu bincike sun bayyana cewa, wani dan bangere na mutanen da ke yin cacar ne kawai, ke samun a cacar, inda akasarin sauran, ke tabka asarar kudadensu da suka zuba a cikin cacar.
An dai jima ana yin caca a kasar, wadda a shekarun baya, ake yi mata wani kallon kan abinda bai dace ba, kamar dai yadda Coci ta alakanta ta, a matsayin hanyar yin arzikin dare daya
Idan za a iya tunawa, bangare na 22 na sashe 236 na kundin dokar aikata manyan laifuka na 1990, Gwamnatin Tarayya ta halasta wasu nau’uka na yin caca, musamman domin ta samar da kanta, kudaden shiga.
Dokar ta fayyace tsakanin wasan kwarewa wanda yake an halasta da kuma wani wasan, na neman sa a, wanda aka haramta.
Wasu nau’ukan na cacar da aka halasta, sun hada da, cacar da ake sayen wani Tikiti domin shiga gasar zamowa Zakara kan wani abu da aka sanya kamar mota ko wani gida da sauransu.
Amma abin takaici, hakan ya sanya cacar ta kara karbuwa ga wasu alummar gari, musamman a tsakanin yaran da suke da kanannan shekaru.
Kazalika, mun fi lura da akasarin nau’ukan cacar da ake yi a kasar, misali wacce a yanzu ake yi kasar kamar ta gasar ta Kwallon Kafa da sauransu, da ake yi, a kafar Internet.
An yi hasashen cewa, rashin aikin yi, sun arzirta a dare daya, matsain tattalin arziki, su ne, kusan hummulhaba’isin da ke sanya wasu mutanen kasar, musamman matasa ke rungumar wannan halin, inda kuma hakan, ke kara haddasa, aikata manyan laifuka.
Muna damu makuka kan yadda wannan halin, ke kara tarwatsa, tarbiyar wasu matasan kasar, da suka rungimi wannan dabi’ar.
A saboda haka, akwai bukatar Gwamnatin Tarayya, ta dauki matakin kan wannan batun.
Fanin cacar gasar wasa ta Nijeriya, ta kasance a kan gaba a Afirka, duba da yadda a kasuwar a 2023 aka samu ribar da kai ta akalla dala biliyan biyu,
Kazalika, duba da yadda a fannin ake samun sama da tiriliyan uku ko kuma sama da haka, cacar gasar wasa ta Nijeriya, sama da shekarun da suka wuce, wannan fannin, sai kara tumbatsa yake yi kasar, wanda haka na faruwa ne, saboda matsin tattalin arziki, karuwar matasa marasa aikin yi da kuma kara bunkasar yin amfani da wayoyin tafi da gidanka.
Ana dai kara ci gaba da samun irin wadannan shagunan da ake gudanar da irin wannan cacar ta gasar wasanni kusan ako wanne tituna da kuma a dandalin sada zumunta, wanda hakan, ya bai matasan kasar da damar, rungumar dabi’ar ta caca, musamman domin su samar wa kansu, da kudaden shiga,
Zamu iya cewa, mun jahilaci cewa, kasancewar yanayin matsalin tattalin arziki da Nijeriya ke fuskanta ne, ya hadda samun karin guraren da ake gudanar da gasar ta cacar wasanni.
A cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa NBS, samun karuwar matasa marasa aikin yi a kasar, ya sanya su daukar matakan da suke ganin ya dace da su, domin su samarwa da rayuwarsu mafita, musamman yadda suke kara rungumar cacar ta gasar wasanni, da suke mata kallon mataki na zuba hannun jari.
An kiyasata cewa, a wannan fannin, ana samaun akalla Naira tiriliyan uku a shekara, wanda kuma ake kara samun ‘yan kasuwa na tallata hajojinsu ta hanyar amfani da kafar sada zumunta, daukar nauyin tallace-tallacen, da suka samu amincewar wasu fitattu.
Wannan ya nuna yadda rahoton Mujallar Lancet ya bayyana matasan da suka rumgumi cacar ke shafe sa’oi 24 suna gudanar da cacar, wadda kuma ke shafar lafiyarsu da barnatar da kudaden da suke yi.
A bangaren mu, tsawon lokacin da ake ci gaba da fuskanta na kangin matsin tattalin arziki a kasar wanda hakan, ya tilatsa wasu matasan yin cacar ta wasanni, abin damuwa ne.
Bugu da kari, yadda wannan batun ke shafar tabin hankalin matasa da ke yin dabi’ar abin damuwa ne, musamman ganin yadda kwararru a fannin kiwon lafiyar ‘yan Adam suka yi gargadin cewar kara samun matasa masu yin dabi’ar a kasar, na kara jefa matasan a cikin matukar damuwa, inda har wasu matasan saboda fusatar rashin samun nasara a dabi’ar, suke kashe kansu ko kuma rungumar tu’ammali, da kayan maye.
Mai makon su rinka zuba kudaden su a halastattun sana’oi, amma sai buge za zuba kuaden, a cacsar gasar wasannin
Duk da ikirarin da irin wadannan kamfanonin na cacar gasar wanni ke yi cewa, suna samar da nishadi da damar samar da ayyukan yi ga matasan ne, ammu mu dai, mun yi ammanar cewa, suna dai kawai amshe ‘yan kudaden matasan ne.
Babu wata tamtama, akwai bukatar a kakabawa fannin da irin wadannan kamfaonin na cacar gasar wasannin, tsauraran matakai.
Kazalika, akwai matukar bukatar Hukumar sa ido kan irin caca ta kasa NLRC wacce kuma ke sa ido kan cacar gasar wasanni ta kara karfafa dokokin yin gasar cacar ta wasanni tare da daukar matakan da suka kamata, ciki har da sanya dokar tallace-tallace da iyakance yawan kudaden da ake zubawa a cikin cacar, kamar dai, yadda ake yi wasu kasashen duniya.
Hakazalika, ya zama wajibi, Gwamnatocin Jihohi su tashi tsaye, wajen samar da tsare-tsaren da matakai da za su hana matasa shiga cikin dabi’ar.
Idan har mahukunta a kasar ba su samar da daukin da ya dace ba, yunkurin matasan na son arzircewa a dare daya, za ta ci gaba da kasancewa, wanda hakan kuma, zai shafi makoyar matasan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arziki gasar wasanni wasu matasan cacar gasar
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
Rayukan al’umma gami da dukiya musamman na ababen hawa na ci gaba da salwanta a Mahadar hanya ta yankin Tipper-garage da ke Dutse-Baupma, da ke kan titin da ya tashi daga garin Dutsen-Alhaji ya nufi garin Bwari, a yankin Birnin Tarayya Abuja.
Titin da ke mastayin tagwaye ya haɗa yankin da garin Jere da ke Jihar Kaduna.
Hanyar na ci gaba da ganin ƙaruwar kwararan motoci a sakamakon ingancinta da kuma karancin matsalar tsaro, idan a ka kamanta ta da babban titi Abuja zuwa Kaduna.
Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027 An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifasAdadin motoci da ke bin titin ya kara dagawa a bayabayan nan a dalilin mummunan cunkushewar hanya da ake fuskanta a garin Zuba Abuja da kuma Madalla da ke Jihar Neja, a sakamakon rufe hannu guda na hanyar biyo bayan fara aikinsa da wani sabon kamfani ke yi, bayan karbe aikin daga kamfanin Bega.
Baya ga motoci na matafiya da ke yawan ratsawa ta hanyar, akwai kuma motocin tifa da ke daukar duwatsu daga kamafanonin fasa duwatsu biyu da ke kusa da mahadar hanyan suna kai wa yankuna daban-daban na Abuja dama kewaye.
Aminiya ta ba da labarin cewa hatsarin mota na baya bayan nan da a ka fuskanta a hanyar su ne wanda ya auku a ranar Asabar 5 ga wannan watan na Afrilu, 2025, inda a ka rasa rayukan mutum biyar, bayan wata babbar mota tirela da ta fito ta kusurwan Bwari ta fuskanci matsalar tsinkewar birki a yayin da ta ke gangarowa daga hayin madatsar ruwa na Usuma dam da ke kan titin.
Tirelar ta taka kekunan adaidaita sahu guda biyar da ke daukar fasija a gefen hanayar, baya ga wani adadi na baburan acaba.
Kwana biyu bayan aukuwar hatsarin, an sake fuskantan wani a ranar Litinin da ta biyo baya inda wata babbar mota irin ta daukar bulo da ke dauke da albasa daga wata jiha ta Arewa ta rasa birki a yayin saukowa daga gangarar hanyar.
Ta buge kekunan kafin ta kife a kusa da wani magudanan ruwa da ke jikin hanyar.
An bada labarin rasa mutum biyu a yayin hatsarin, baya ga wasu da su ka tsira da raunuka.
Asarar rayuka da ta dukiya da muka yi — Masu tukin adaidaita sahu
Malam Fahad Musa na cikin shugabannin kungiyar ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin Keken Adaidaita sahu da ke aiki a wurin.
Ya ce hatsarin farko ya faru ne da misalign karfe 7 na dare inda ya ce sun rasa mambobinsu uku, sai kuma dan acaba guda, a yayin da mutum na biyar din kuwa ya rasa ransa ne a dalilin harbinsa da bindiga da ake zargin wasu da suka taho cikin ayarin motoci suka yi, kamar yadda majiyoyi daban-daban suka shaidawa Aminiya.
Shugaban na ’yan yuniyon ya shaida wa wakilinmu a yayin ziyara a wajen cewa an kuma rasa kekune biyar a yayin hatsarin bayan motar ta bi ta kansu.
Ya ce faduwar motar ta farko ta yi sanadiyyar rufe hannu guda sannan ba a kai ga cire ta ba sai bayan hatsari na biyu a ranar Litinin.
Ya ce, a lokacin da ake kokarin zakulu mutane da suka mutu da kuma wadanda suka yi raunukan daga karkashin ababan hawan a ranar Asabar, an rufe daukacin tagwayen titin biyu da lamarin ya kai ga jawo takaddama bayan ayarin jami’an tsaro sun bulla ta wajen.
Wani da ya shaidi lamarin, ya shaida wa Aminiya cewa, a lokacin da ayarin motocin suka bullo, wani babba a cikin tawagar ya fito daga cikin mota tare da neman da a bude masu daya hanyar, amma sai ’yan asalin al’ummar yankin suka ki amincewa da bukatar hakan.
Ya kara da cewa, matasan sun bi motocin ayarin da jifa bayan sun kutsa ta daya hanyar da nufin wucewa, kuma a nan ne sai wasu daga cikin jami’an tsaron suka yi harbi cikin iska, a yayin da wani kuma ya harbi daya daga cikin matasa ’yan asalin yankin mai suna Timothy John, da ya mutu nan take.
Bayan nan, ayarin sun wuce da motocinsu cikin hanzari, kamar yadda aka bayyana wa Aminiya.
A yayin zantawarsa da Aminiya shugaban n ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin adaidaita sahu ya ce, daya daga cikin direbobinsu mai suna Yusuf Auwal na cikin wadanda harsashin bindiga ya bi ta jikinsa.
Ya ce, bayan nan an garzaya da shi zuwa garinsu inda yake cigaba da jinya a yanzu.
Babban Kwamandan Hukumar Kare Hadurra na FRSC mai kula da yankin Dutsen-Alhaji, Mista Luka Wuna, ya tabbatar da faruwan haduran biyun, da kuma rasa rayukan, a yayin zantawarsa da wakilinmu a kan lamari.
Akwai bukatar ilimantar da direbobin Tifa
Binciken Aminiya ya bayyanan cewa, matsalar da tifofi ke samu ta shanyewar burki a yayin da suka ɗauko kaya kuma suka sukwano gangarar da daga ita sai marabar titin ita ce a mafi yawan lokaci ke haddasa munanan hadurra a wannan mahada.
Da yawan direbobin tifa matasa ne da basu san dokokin tuki ba sannan kuma suna tukin da ganganci tamkar suna tuka kananan motoci.
Don haka mafi yawa ba sa kula da yadda suke shawo wannan gangara ta la’akari da cewa, burkin tifa iska ce.
Wani masanin harkokin sufuri da ba ya son a ambaci sunansa ya ba da shaara cewa, ya kamata hukumomin da abin ya shafa su rinka shirya wa direbobin musamman na Tifa bita kan ka’idojin tuki da alamomin hanaya da kuma hatsarin da ke tattare da burkin mota mai dauke da iska.
Abinda ke jawo hatsari a wajen
Malam Anas Mu’azu na cikin ma’aikatan tattara haraji na Karamar Hukumar Bwari da ke ba da tikiti a wajen.
Ya ce, yawancin direbobi da ke fuskantar hatsarin baki ne da ke bi ta gangaren hanyar ba tare da cikakken masaniya a kan yadda wajen yake ba.
Ya ce, ”wutar ba da umarnin wucewa a wajen da ke da kusurwa 4 na bukatar tsayawar mota na wani lokaci a duk ta inda ta fito saboda dogon layi da motoci ke yi, sannan indan wutar ta haska don wucewa, adadi kadan ne na motoci ke iya wucewa kafin ta sake bukatar tsayar da mota,” in ji shi.
Malam Anas ya kara da cewa yawancin bakin direbobi da ke bin hanyar ba su da masaniya a kan tsarin wutar da kuma yanayin hanyar kasancewar babu allunan alamomi na hanya da ke fadakarwa a kan titin.
Ya ce, haka kuma a baya an cire kunyar kan titi da ke sa motoci rage gudun mota. ”A baya akwai kunyar titi na rage gudun da adadinsu ya kai kamar guda biyar, amma sai a ka cire su a lokaci guda ta hanyan kankare su daga kan hanyar,” in ji shi.
Ya ce, ko da Ministan Birnin Abuja Mista Nyesom Wike ya ba da aikin sake gina hanyar a bayabayan nan, ba a maida kunyar titin ba, har zuwa lokacin da haduran baya-bayan nan su ka auku..
Yadda za a magance matsala —Masu Tifa
Haka kuma Aminiya ta zanta da daya daga shugabannin masu motocin tifa da kuma harkar sayar da duwatsu daga kamfanoni biyu na fasa dutsi da ke yankin mai suna Kwamred Ose Idasho inda ya ba da shawarwaari kan yadda ya ke ganin za a magance yawaitar haduran, da ya ce sun bayar a yayin wani zama na musamman da Jami’an Hukumar Magance Hadurra ta FRSC a yankin.
Ya ce, “abu na farko shi ne bukatar a sa alamomin hanya tun daga kamar kilo mita uku kafin mahadar hanyar da zai rika sanar da direba hatsarin wajen tare da bukatar da ya yi takatsantsan.
“Sai kuma a sa abubuwa da ke sa rage gudun mota na kunyar hanya samfurin roba ba na siminta ba, da zai rika yin kara idan direba ya yi yunkurin yin gudu sosai. Hakan zai kara wa direba karsashi ko da ya fara yin gyangyadi.
“Mun kuma bukaci jami’an na FRSC da nemi dauki daga Hukumar Kula da Gine-gine ta Abuja kan su kawar da wuraren da ke sa mutane na tsayawa ta wurin, tare da mayar da shi sarari, sai kuma samar da wurearen yin lodi da kuma hana yin lodi a gefen titin.
“Haka kuma akwai bukatar a gyara wasu daga cikin fitilun ba da hannu da suka daina yin aiki, kamar wanda ya shiga ta bangaren Bamuko ta inda motocin tifa ke shiga da kuma yawan fita.
Sai kuma uwa-uba a gina gadar sama a wajen da zai rage girman gangarowar motoci da ke fitowa ta kusurwar Bwari ko DutsenAlhaji inda motocin za su bi ta saman gada,” in ji jagoran masu motocin tifa.
Ya kamata a gina gadar sama
Shi ma a zantawarsa da Aminiya, Sakataren Hakimin yankin na Dutse-Baupma mai suna Simon Luka da ya yi bayani a madadin hakiminsu, ya ce, hatsarin motoci a wajen ya jima yana jawo masu fargaba da kuma asarar rayuka da dukiya.
Ya buƙaci Ministan Birnin Tarayya Mista Nyesom Wike da ya taimaka wajen yin aikin gadar sama a wajen don magance matsalar.
Ya ce, tarihin farawar matsalar ba za ta gaza shekara 20 bayan an yi aikin hanyar.
Ya ce, matashin da aka kashe bayan jami’an tsaro sun buɗe wuta a wajen mai suna Timothy John, bai wuce shekara 20 ba kuma lamarin ya faru ne kasa da mako guda bayan mai gidansa ya yaye shi daga aikin walda da ya ke yi, inda yake shirin buɗe na kansa.
Ya kara da cewa, “sai dai har zuwa lokacin ziyarar nan babu wata ta’aziyya ko ta jaje da muka samu daga jamiu’an tsaro ko kuma hukuma, kan mutuwar matashin.”
Aminiya ta tuntubi Babbar Jami’ar Hulda da Jama’a a Sakatariyar da ke Kula da Sufuri a yankin Birnin Tarayya Abuja mai suna Misis Lecita Wogu, inda ta buƙaci lokaci don yin tsokaci a kan lamarin.