Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron Kan Iyakar Kasashen Biyu
Published: 10th, April 2025 GMT
Sojojin kasa na kasashen Iran ta Armenia sun fara atisayen soje na hadin guiwa a tsakaninsu, don kyautata tsaro na kan iyakar kasashen biyu na kuma tsawon kwanaki biyu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ne suke jagorantar wannan atisayen.
Burgediya Janar Sayyid Mortaza Mira’in babban hafsan sojojin kasa na IRGC ya bayyana cewa, wannan atisayennn yana nuna irin yadda sojojin IRGC suke da shirin kare kasar daggga duk wata barazana. Da kuma abota da kyautata makobtaka da kasashe mmmakobta.
Labarin ya kara da cewa ana gudanar da rawan dajin ne a kan kan iyakar kasashen biyu na nordooz.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
Sojojin mamayar Isra’ila sun mayar da cibiyoyin bada agaji zuwa filin yakin kashe Falasdinawa a Zirin Gaza
Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da mayar da cibiyoyin bayar da agajin jin kai zuwa wani mummunan tarko na aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa, wanda hare-haren baya-bayan nan da suka kai kan fararen hula sunka yi sanadiyar hasarar rayuka da dama tare da jikkata wasu masu yawa. Wannan mummunan al’amari ya janyo gargadin Majalisar Dinkin Duniya cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana kai wa masu fama da yunwa hari.
Jiragen yakin gwamnatin mamayar Isra’ila da kuma amfaniu da manyan bindigogi suna barin wuta kan mai uwa da wabi kan Falasdinawa da suka taru domin karbar kayan jin kai. Gwamnatin mamayar Isra’ila ta bullo da wannan sabon hanya ce domin kashe Falasdinawa a matsayin tarko ga Falasdinawa, kuma ba ta sha yin ci gaba da wannan ta’asa domin babu mai iya hana ta ko tofin yin Allah wadai da ita.
Wani magidanci da ya dawo daga karbar agaji da ‘ya’yansa biyu a Khan Yunus, ya fuskanci bude wuta inda dansa guda ya yi shahada dayan kuma yana nan rai kwai-kwai mutum kwai-kwai.
A cewar wata sanarwa da ma’aikatar harkokin cikin gida da tsaron kasa a zirin Gaza ta fitar, ta jaddada cewa: Daruruwan Falasdinawa ne suka yi shahada sakamakon harsashin sojojin mamayar Isra’ila a wuraren bada agajin jin kai zuwa yanzu.