Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
Published: 10th, April 2025 GMT
Kasashen China da Tarayyar Turai sun maida martani kan kudaden fiton da Amurka ta kara masu.
Kamfanin dillancin labaran Rauter ya bayyana cewa kasashen Turai 27 sun kara kashi 25% ga wasu zababbun kayakin kasar Amurka masu shigowa kasashen su. Wannan dais hi ne maida martani na farko wanda kasashen turan suka yi tun bayan da gwamnatin shugaba Trump ta kara kudaden fito ga kasashen duniya da dama wadanda suka hada da China da kuma kasashen turai EU.
Labarin ya kara da cewa karin kudaden fiton sun shafi motoci da karfe da kuma karfen alminium ne da suke shigo da su daga kasar ta Amurka ne. Banda haka karin kudaden fiton sun shafi kayakin abinci wadanda suka hada da waken soya, kayan zaki, shinkafa lemun zaki, almonds, taba da kuma wasu ababen hawa da kuma Kannan kwalekwale.
Jimillar kayakin da abin ya shafa zai kai Uro billiyon 22.1. sai dai wannan bai kai Euro billiyon 26 wanda gwamnatin Amurka ta karawa kasashen na turai ba.
Labarin ya kammala da cewa sabon kudaden fito na kayakin Amurkan zai fara aiki a ranar talata 15 ga watan Afrilun da muke ciki, wasu kuma 16 ga watan Mayu da kuma wasu a ranar 1 ga watan Decemba karshen wannan shekara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar
Sudan ta yaba da kokarin zaman lafiya da Amurka da Saudiyya suka yi na dakatar da zubar da jini a kasar.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a shafin X, Majalisar Mulkin Sojan Sudan ta yi maraba da “kokarin Saudiyya da Amurka na kawo zaman lafiya mai ga Sudan.”
Ta gode wa Washington da Riyadh saboda “sha’awarsu da kuma ci gaba da kokarinsu na dakatar da zubar da jinni a Sudan” kuma ta tabbatar da shirin Sudan na yin tattaunawa da kasashen biyu “don cimma zaman lafiyar da al’ummar Sudan suka dade suna jira.”
Wannan sanarwar ta zo ne jim kadan bayan da Shugaba Donald Trump ya ce Amurka “za ta fara dubi lamarin Sudan” bisa bukatar Yarima Mohammed bin Salman na Saudiyya.
Abdel Fattah al Burhan, shugaban majalisar kuma babban hafsan sojojin, shi ma ya gode wa yarima na Saudiyya da Trump da kansa a shafinsa na X.
Sojojin Sudan da rundunar kaidaukin gaggawa ta (RSF) na rikici tsakaninsi tun daga ranar 15 ga Afrilu, 2023, lamarin da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallinsu.
Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM) ta kiyasta cewa sama da fararen hula 140,000 ne suka tsere daga Al Fasher, babban birnin Arewacin Darfur, da kuma jihar Kordofan ta Arewa saboda hare-haren RSF tun daga karshen watan Oktoba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka November 19, 2025 Sojojin Yemen Suna Da Makami Mai Linzami Da Babu Mai Makamancinsa Sai Iran November 19, 2025 Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar November 19, 2025 Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta A Gaza Kusan Sau 400 November 19, 2025 Kotu A Gabon Ta Yanke Hukuncin Dauri A Kurkuku Kan Jami’an Tsohuwar Gwamnatin Kasar November 19, 2025 Kasar Maziko Tayi Watsi Da Shirin Trump Na Kai Harin Soji Kan Iyakar Kasar. November 19, 2025 Iran Ta yi Gargadi Kan Kada Kudurin Amurka Da MDD Ta Amince Da Shi Ya Tauye Hakkin Falasdinawa November 19, 2025 kungiyar Hadin Guiwa Ta SCO Ta yi Watsi Da Adawar Da Kasashen Turai Ke Nuna wa Kasar Iran November 19, 2025 Majalisa wakilai A Najeriya Ta Bukaci Gwamnati Ta Sake Dabarun Yaki Da Ta’addanci November 19, 2025 Kimanin Falasdinawa 22 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila A Ainul Hilwa November 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci