HausaTv:
2025-11-21@10:04:35 GMT

Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka

Published: 10th, April 2025 GMT

Kasashen China da Tarayyar Turai sun maida martani kan kudaden fiton da Amurka ta kara masu.

Kamfanin dillancin labaran Rauter ya bayyana cewa kasashen Turai 27 sun kara kashi 25% ga wasu zababbun kayakin kasar Amurka masu shigowa kasashen su. Wannan dais hi ne maida martani na farko wanda kasashen turan suka yi tun bayan da gwamnatin shugaba Trump ta kara kudaden fito ga kasashen duniya da dama wadanda suka hada da China da kuma kasashen turai EU.

Labarin ya kara da cewa karin kudaden fiton sun shafi motoci da karfe da kuma karfen alminium ne da suke shigo da su daga kasar ta Amurka ne.  Banda haka karin kudaden fiton sun shafi kayakin abinci wadanda suka hada da waken soya, kayan zaki, shinkafa lemun zaki,  almonds,  taba da kuma wasu ababen hawa da kuma Kannan kwalekwale.

Jimillar kayakin da abin ya shafa zai kai Uro billiyon 22.1. sai dai wannan bai kai Euro billiyon 26 wanda gwamnatin Amurka ta karawa kasashen na turai ba.

Labarin ya kammala da cewa sabon kudaden fito na kayakin Amurkan zai fara aiki a ranar talata 15 ga watan Afrilun da muke ciki, wasu kuma 16 ga watan Mayu da kuma wasu a ranar 1 ga watan Decemba karshen wannan shekara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa

An shiga jimami a garin Zugai da ke Ƙaramar Hukumar Roni ta Jihar Jigawa, bayan da wani tankin ruwa ya faɗo tare yin sanadin rasuwar mutum da jikkata wasu.

Daga cikin waɗanda suka rasu har da wata mace mai juna biyu.

An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026

Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya auku ne kwana uku bayan shugaban Ƙaramar Hukumar, ya raba ruwa ga masu sana’r sayar da ruwa, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin wasu mutane.

Tankin ruwa, wanda ke amfani da hasken rana wajen samar da ruwa, ya fashe yayin da mutane da yawa suka taru a ƙasa domin ɗibar ruwa.

Shaidu sun ce tankin ya rushe ba zato ba tsammani, inda mutum uku suka mutu nan take, waɗanda suka jikkata aka garzaya da su asibiti.

Shugaban Majalisar Ƙaramar Hukumar Roni, Dokta Abba Ya’u Roni, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya tabbatar da mutuwar mutum huɗu.

Dokta Abba, ya ce fashewar tankin ta faru ne sakamakon iska mai ƙarfi wadda ta turo tankin ya faɗo kan mutane.

Ya ƙara da cewa: “Na umarci mataimakina da jami’an majalisa su kai ziyara ƙauyen don tabbatar da cewa duk waɗanda suka ji rauni an kula da su.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Wasu Kasashe Bakwai Sun Mayar Da Martani Kan Hudurin IAEA Kan Kasar Iran
  • IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Kasashen Iran Da Malesiya Sun Rattaba Hannu Kan Jarjejeniyar Fadada Dangantakar Addini
  • AU ta yi Allah-wadai da tsoma bakin kasashen waje a harkokin tsaron Afirka
  • Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  •  kungiyar Hadin Guiwa Ta SCO Ta yi Watsi Da Adawar Da Kasashen Turai Ke Nuna wa Kasar Iran
  • Saudiyya za ta kara hannun jarinta a Amurka zuwa dala tiriliyan daya
  • Iran: An Bayyana Taron Gundumomin Dake Gabar Ruwan ” Caspian” Da Cewa Yana Bunaksa Alakar Kasashen Yankin