Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
Published: 10th, April 2025 GMT
Kasashen China da Tarayyar Turai sun maida martani kan kudaden fiton da Amurka ta kara masu.
Kamfanin dillancin labaran Rauter ya bayyana cewa kasashen Turai 27 sun kara kashi 25% ga wasu zababbun kayakin kasar Amurka masu shigowa kasashen su. Wannan dais hi ne maida martani na farko wanda kasashen turan suka yi tun bayan da gwamnatin shugaba Trump ta kara kudaden fito ga kasashen duniya da dama wadanda suka hada da China da kuma kasashen turai EU.
Labarin ya kara da cewa karin kudaden fiton sun shafi motoci da karfe da kuma karfen alminium ne da suke shigo da su daga kasar ta Amurka ne. Banda haka karin kudaden fiton sun shafi kayakin abinci wadanda suka hada da waken soya, kayan zaki, shinkafa lemun zaki, almonds, taba da kuma wasu ababen hawa da kuma Kannan kwalekwale.
Jimillar kayakin da abin ya shafa zai kai Uro billiyon 22.1. sai dai wannan bai kai Euro billiyon 26 wanda gwamnatin Amurka ta karawa kasashen na turai ba.
Labarin ya kammala da cewa sabon kudaden fito na kayakin Amurkan zai fara aiki a ranar talata 15 ga watan Afrilun da muke ciki, wasu kuma 16 ga watan Mayu da kuma wasu a ranar 1 ga watan Decemba karshen wannan shekara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: An Bayyana Taron Gundumomin Dake Gabar Ruwan ” Caspian” Da Cewa Yana Bunaksa Alakar Kasashen Yankin
Fira ministan jamhuriyar Kalmykia mai kwarya-kwaryar cin gashin kai a tarayyar Rasha, Utshir Janibinov ya fada wa manema labaru a wurin taron gwamnonin gundumomin dake gabar ruwan “Caspian” cewa; Taron da aka yi wanda shi ne irinsa na farko yana da tasiri mai kyau wajen bunkasa alaka a tsakanin gundumomin gabar ruwan “Caspian”.
Taron na gwamnonin gundumomin da suke a gabar ruwan “Caspian” an yi shi ne dai a garin Rasht a gundumar Gilan dake nan Iran.
Mataimakin Fira ministan jamhuriyar Kalmykia ta tarayyar Rasha, ya bayyana jin dadinsa na halartar wannan taron a nan Iran.
A Yau Talata ne dai aka bude wannan taron wanda aka bai wa taken: ” Tekun Caspian A Matsayin Wata Gada Ta Bunkasa Alaka A Cikin Yanki.” Kuma zai zai gaba har zuwa kwanaki biyu anan gaba.
A wani gefen mataimakin ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, ana sa ran halartar shugaban kasar Rash Vladmir Putin zuwa taron kungiyar kasashen dake gabar ruwan “Caspian” da za a yi a nan Iran a nan gaba.
Mataimakin ministan harkokin wajen na Iran ya fada wa kamfanin dillancin labarun “RIA Novosti” cewa; Ziyarar shugaba Valadmir Putin zuwa Iran domin halartar taron kungiyar kasashen gabar tekun “Caspian” yana cikin jadawalin aiki.
Sai dai mataimakin ministan harkokin wajen na Iran bai bayyana wa’adin gudanar da wannan taron ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Nijar: An Dakatar Da Ayyukan Kungiyoyin Agaji Da Dama November 18, 2025 Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahada Sanadiyyar Harin Sojojin “Sahayoniya A Garin Bint-Jubail November 18, 2025 Brazil: Al’ummun Yankunan Karkara Na Amazon Sun Yi Gangami A Wurin Taron MDD Akan Muhalli November 18, 2025 Sojojin Najeriya Sun Karyata Cewa “ISWAP” Ta Kashe Wani Babban Jami’i Mai Mukamin Birgediya November 18, 2025 Najeriya ta Fara tattaunawa da Amurka kan zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi November 18, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Amincewa Da Kudurin Amurka Da Kwamitin Tsaro Ya yi Kan Gaza November 18, 2025 Afrika ta Kudu Ta yi Gargadi Game Da Duk Wani Yunkuri Na Fitar Da Falasdinawa Daga Yankin Gaza November 18, 2025 Tsohon jami’an MDD Yayi Tir Da Amincewa Da Kudurin Amurka A Kwamitin Sulhu Kan Gaza November 18, 2025 Mataimakin Shugaban Iran Na Daya Ya Gana Da Prime Ministan Rasha A Birnin Mosko November 18, 2025 Ministan tsaron Iran na Ziyara a UAE don karfafa dangantakar tsaro tsakanin kasashen yankin November 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci