Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
Published: 10th, April 2025 GMT
Kasashen China da Tarayyar Turai sun maida martani kan kudaden fiton da Amurka ta kara masu.
Kamfanin dillancin labaran Rauter ya bayyana cewa kasashen Turai 27 sun kara kashi 25% ga wasu zababbun kayakin kasar Amurka masu shigowa kasashen su. Wannan dais hi ne maida martani na farko wanda kasashen turan suka yi tun bayan da gwamnatin shugaba Trump ta kara kudaden fito ga kasashen duniya da dama wadanda suka hada da China da kuma kasashen turai EU.
Labarin ya kara da cewa karin kudaden fiton sun shafi motoci da karfe da kuma karfen alminium ne da suke shigo da su daga kasar ta Amurka ne. Banda haka karin kudaden fiton sun shafi kayakin abinci wadanda suka hada da waken soya, kayan zaki, shinkafa lemun zaki, almonds, taba da kuma wasu ababen hawa da kuma Kannan kwalekwale.
Jimillar kayakin da abin ya shafa zai kai Uro billiyon 22.1. sai dai wannan bai kai Euro billiyon 26 wanda gwamnatin Amurka ta karawa kasashen na turai ba.
Labarin ya kammala da cewa sabon kudaden fito na kayakin Amurkan zai fara aiki a ranar talata 15 ga watan Afrilun da muke ciki, wasu kuma 16 ga watan Mayu da kuma wasu a ranar 1 ga watan Decemba karshen wannan shekara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
A ranar Alhamis, 20 ga watan Nuwamban 2025, ake sa ran Majalisar Wakilan Amurka za ta gudanar da zama na musamman domin bincikar zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya.
Kwamitin Majalisar Wakilan kan Afirka ya sanya ranar domin bitar fasalin da Shugaba Donald Trump ya yi kwanan nan na sanya Nijeriya a matsayin kasar da ake sa wa ido na musamman, CPC, kan zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi.
Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a KebbiGidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa, an gayyaci mambobin Kwamitin Harkokin Waje na majalisar, wanda aka shirya za a yi tattaunawar da misalin ƙarfe 11:00 na safe a Ɗaki mai lamba 2172 na Ginin Ofishin Gidan Rayburn, sannan kuma za a iya kalla ta intanet kai-tsaye, wanda wakili Chris Smith (R-NJ) ne zai jagoranta.
Za a gabatar da kwamitoci biyu na shaidu, ciki har da manyan jami’an Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da shugabannin addinai na Nijeriya.
Gayyatar tana cewa, “Ana roƙonku da girmamawa da ku halarci zaman sauraron ƙararraki na Kwamitin Harkokin Waje da ƙaramin kwamiti kan Afirka zai gudanar da shi da ƙarfe 11:00 na safe a ɗaki mai lamba 2172 na ginin Ofishin Rayburn House.”
Trump ne ya fara sanya Nijeriya a matsayin kasae da ake sa wa ido na musamman, CPC a shekarar 2020, kafin magajinsa, Shugaba Joe Biden, ya cire ƙasar daga jerin sunayen bayan ya kayar da Trump.
Masu sauraron za su haɗa da Babban Jami’in Ofishin Harkokin Afirka, Jonathan Pratt, da Mataimakin Mataimakin Sakatare na Ofishin Dimokuradiyya, ’Yancin Dan’Adam, da Aiki, Jacob McGee.
Za a yi zaman tattaunawa ta biyu da Daraktan Cibiyar ’Yancin Addini, Ms Nina Shea; Bishop Wilfred Anagbe na Makurdi Catholic Diocese a Nijeriya; da Ms Oge Onubogu ta Cibiyar Dabaru da Nazarin Ƙasashen Duniya.
Ana sa ran zaman tattaunawa ta majalisar zai sake duba girman zargin cuzguna wa masu wani addini a Nijeriya.
Za a kuma yi nazarin irin martanin manufofi da za a iya ɗauka, ciki har da takunkumin da aka yi niyyar ƙaƙabawa da taimakon jinƙai, da haɗin gwiwa da hukumomin Nijeriya don hana ƙarin tashin hankali.
Za a kuma gabatar da ƙudirin a gaban Majalisar Dattawan Amurka, wanda Sanata Ted Cruz ya ɗauki nauyinsa.