HausaTv:
2025-12-14@20:38:36 GMT

Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka

Published: 10th, April 2025 GMT

Kasashen China da Tarayyar Turai sun maida martani kan kudaden fiton da Amurka ta kara masu.

Kamfanin dillancin labaran Rauter ya bayyana cewa kasashen Turai 27 sun kara kashi 25% ga wasu zababbun kayakin kasar Amurka masu shigowa kasashen su. Wannan dais hi ne maida martani na farko wanda kasashen turan suka yi tun bayan da gwamnatin shugaba Trump ta kara kudaden fito ga kasashen duniya da dama wadanda suka hada da China da kuma kasashen turai EU.

Labarin ya kara da cewa karin kudaden fiton sun shafi motoci da karfe da kuma karfen alminium ne da suke shigo da su daga kasar ta Amurka ne.  Banda haka karin kudaden fiton sun shafi kayakin abinci wadanda suka hada da waken soya, kayan zaki, shinkafa lemun zaki,  almonds,  taba da kuma wasu ababen hawa da kuma Kannan kwalekwale.

Jimillar kayakin da abin ya shafa zai kai Uro billiyon 22.1. sai dai wannan bai kai Euro billiyon 26 wanda gwamnatin Amurka ta karawa kasashen na turai ba.

Labarin ya kammala da cewa sabon kudaden fito na kayakin Amurkan zai fara aiki a ranar talata 15 ga watan Afrilun da muke ciki, wasu kuma 16 ga watan Mayu da kuma wasu a ranar 1 ga watan Decemba karshen wannan shekara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 

Akalla mutanen 11 ne suka mutu, wasu 29 suka jikkata, a yayin wani hari da aka kai a bakin tekun  Bondi Beach da ke birnin Sydney na ƙasar Ostireliya. 

’Yan bindiga sun kai harin ne a yayin da dubban jama’a ne suka taru a bakin teku domin halartar wani biki mai suna ‘Chanukah by the Sea’, wanda ke nuna fara shagulgulan Yahudawa na Hanukkah.

Rahotanni sun ce wani mutum da ake zargin ɗaya daga cikin masu harin ya mutu, yayin da wani kuma ke cikin mawuyacin hali a asibiti. ’Yan sanda biyu na cikin mutanen da suka jikkata.

Hukumomin Ostireliya sun bayyana lamarin a matsayin harin ta’addanci, tare da jaddada cewa an shirya shi ne domin kai wa al’ummar Yahudawa hari a ranar farko ta bukukuwan Hanukkah.

Taɓarɓarewar rashin tsaro ya nuna rashin shugabanci na gari — Obi Akwai fargaba kan noman ranin bana

Firaministan Ostireliya, Anthony Albanese, ya yi Allah-wadai da harin, tare da cewa mummunan ta’addanci da aka aikata ya wuce tunanin ɗan adam.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha
  • Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani
  • Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja
  • Kasashen AES zasu kafa bankin dogaro da kai
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Waiwaye Adon Tafiya: Manyan Nasarorin Da Aka Cimma A Dangantakar Kasashen Afirka Da Sin A 2025
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026