An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno
Published: 11th, November 2025 GMT
Rundunar sojin Operation Hadin Kai (OPHK) da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas ta sake samun nasara bayan ta ceto mutane 86 da kuma kama wasu mutum 29 da ake zargi da samar wa ’yan ta’adda kayayyaki a Jihar Borno.
A cewar sanarwar da Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Litinin, an gudanar da wannan samame ne a ranar 9 ga Nuwamba, bayan samun sahihan bayanan sirri da suka tabbatar da cewa ’yan ta’adda suna garkuwa da fararen hula a kan hanyar Buratai–Kamuya.
Sojojin Bataliyar Musamman ta 135 da ke ƙarƙashin Sashe na 2 na OPHK sun yi artabu da mayakan Boko Haram da ISWAP a Dutsen Kura, inda suka fatattake su bayan fafatawar da ta gudana har zuwa yankin Mangari.
Sanarwar ta bayyana cewa an gano mafakar ’yan ta’adda guda 11, sannan an kubutar da maza, mata da yara 86 da aka garkuwa da su.
Kayayyakin da aka kwato sun haɗa da bindigar AK-47 guda ɗaya, harsasai 73, jigidar harsashi 5, motoci 5, babura 5, kekuna 8 da kuma babura masu ƙafa uku guda 2.
A wani samame na daban a Mangada, dakarun sun kama mutum 29 da ake zargi da kai wa ’yan ta’adda kayayyaki, tare da kwace motocin ɗaukar kaya guda 2 da babura masu ƙafa uku cike da man fetur da man injin sama da lita 1,000.
Laftanar Kanar Uba ya ce an gudanar da duka ayyukan ba tare da asarar rai ko rauni a ɓangaren sojoji ba, inda babban kwamandan rundunar ya yabawa jarumtar dakarun tare da buƙatar su ci gaba da hana ’yan ta’adda samun damar shakatawa a duk faɗin yankin Arewa maso Gabas.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda jihar Borno yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
A bana ne ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da Sinawa suka yi da mamayar dakarun kasar Japan da yakin duniya na kin tafarkin murdiya, gami da kawo karshen mulkin mallakar kasar Japan a yankin Taiwan da dawo da shi kasar Sin. Kwanan nan ne CMG wato babban rukunin gidajen radiyo da talabijin na kasar Sin ya wallafa jerin wasu rahotannin talabijin guda biyar dangane da batun dawowar Taiwan kasar Sin.
’Yan jarida ma’aikatan CMG ne suka dauki rahotanni da bidiyo a yankin Taiwan, inda suka yi amfani da kwararan shaidun tarihi, don mayar da martani ga wasu kalaman karya da ke cewa wai “matsayin Taiwan ba shi da tabbas”, tare kuma da bankado markarkashiyar mahukuntan jam’iyyar DPP na yankin Taiwan ta yabawa da mulkin mallaka da Japan ta yi da boye gaskiyar tarihi.
Rahotannin na talabijin sun samu babban yabo daga bangarori daban-daban na yankin Taiwan, inda jama’ar yankin ke kira ga mahukuntan Taiwan, da su mutunta gaskiyar tarihi, da daina yaudarar jama’ar Taiwan. (Murtala Zhang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA