Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170
Published: 11th, November 2025 GMT
Wannan faɗa na daga cikin mafi muni a watannin baya-bayan nan, yayin da ƙungiyoyin biyu ke fafatawa kan ikon hanyoyin kamun kifi, da hanyoyin fasa ƙwauri a yankin Tafkin Chadi.
Masana harkokin tsaro sun bayyana damuwa cewa ISWAP na iya kai farmakin ramuwar gayya a makonni masu zuwa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Ban ɓata zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya taɓa zargin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da ƙirƙiro Boko Haram.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sanata Sheriff ya bayyana labarin a matsayin ƙarya mara tushe.
Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar NajeriyaYa ce bai taɓa yin wata hira ko yi wa wani bayani da ya shafi Shettima game da kafa Boko Haram ba.
“Wannan labari ƙarya ne gaba ɗaya, kuma an shirya shi ne domin rikita jama’a da kawo rabuwar kai,” in ji sanarwar.
Sheriff, wanda tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya ce waɗanda suka yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin rage ƙimarsa da kuma ɓata gudunmawar da yake bayarwa wajen samar da zaman lafiya da haɗin kai a Jihar Borno da Najeriya baki ɗaya.
Ya ce ya umarci lauyoyinsa su gano waɗanda suka yaɗa labarin tare da ɗaukar matakin shari’a a kansu.
“Idan ba a gaggauta goge wannan labari daga kafafen da suka yaɗa shi ba, zan ɗauki matakin shari’a,” in ji Sheriff.
Sanata Sheriff, ya roƙi ’yan Najeriya da kafafen watsa labarai da su yi watsi da labarin, tare da bin gaskiya da adalci wajen yaɗa bayanansu.