PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
Published: 2nd, August 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya ce farin jinin jam’iyyar adawa ta PDP ya dusashe a jihar.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martanin da wasu jam’iyyun adawa suka yi, wajen zargin gwamnatin jihar da rashin bayyana yadda ta ke kashe kuɗaɗen da aka ware wa ilimi, lafiya, da gine-gine.
Dungurawa, ya ce waɗannan zarge-zargen siyasa ce kawai, ba su da tushe ko makama.
Ya ce waɗanda ke sukar gwamnati su ne suka gaza lokacin da suka yi mulki a Kano.
“Da farko, muna gode musu da suka amince muna aiki. Amma muna tunatar da su cewa sun yi shekara takwas suna mulki amma ba su bar wani abin a-zo-a-gani ba,” in ji Dungurawa.
Ya zargi gwamnatocin baya da yin ayyukan da ba su da tasiri, ba tare da duba buƙatun al’umma ba.
“Misali duba gadar ƙasa da suka yi a Dangi. Ba ta da wani amfani. Babu cunkoso a wajen da zai sa a gina irin wannan. Kawai sun zuba kankare ne ba tare da wata manufa ba,” in ji shi.
Dungurawa, ya ce a ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, gwamnatin NNPP ta mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar gyaran tituna da gina gadoji don sauƙaƙa zirga-zirga a jihar.
“Yanzu haka, ramuka ƙadan za ka ga ni a titunan Kano. Titunanmu sabbi ne, alamomin titi a bayyane suke, fitilun titi suna aiki.
“Wannan yana nuna cewa masu kishin jihar sun karɓi ragamar mulki,” in ji shi.
Ya kuma kare yadda gwamnati ke biyan fansho, inda ya bayyana cewa an riga an biya Naira biliyan 27 daga cikin Naira biliyan 48 da gwamnatin jihar ta gada a matsayin bashi.
“A cikin shekara biyu kacal, mun biya Naira biliyan 27 sannan an biya biliyan 22, kuma za a biya wata biliyan biyar a watan Disamba.
“Wannan ya nuna irin yadda muke tafiyar da gwamnati da gaskiya,” in ji shi.
Game da maganar da wasu ‘yan adawa ke yi cewa jam’iyyunsu na ƙara ƙarfi, Dungurawa ya yi watsi da hakan.
“Wasu daga cikinsu ko a gidajensu ba za a goyi bayansu ba. PDP ba ta da wani ƙarfi. A zahirin gaskiya, mutuwa ta ke ƙara yi. Shugabanninta ba su da haɗin kai kuma son kansa yake yi,” in ji Dungurawa.
Bayan taɓo batun haɗakar ADC, Dungurawa ya ce hakan na nuna rikicin da ke cikin PDP.
“Idan har ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP yana shirin komawa wata jam’iyya, me hakan ke nunawa?
“Yana nuna cewa jam’iyyar ba ta da tsari ko jagoranci. ‘Yan siyasa masu kishin ƙasa sun riga sun bar jam’iyyar tuntuni,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaJami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.
Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”
“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”
Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.