Jihar Sakkwato ta ciyo bashin N70.4bn N70.4bn domin inganta kiwon lafiya
Published: 2nd, August 2025 GMT
Bankin Raya Ci-gaban Afirka (AfDB) ya amince da ba wa Gwamnatin Jihar Sakkwato bashin Naira biliyan 70.4 domin inganta fannin kiwon lafiya.
Wannan shiri na da nufin bunƙasa fannin kiwon lafiya da ingancinsa, da kuma cike giɓin da ake da shi a ɓangaren a Jihar Sakkwato, a cewar AfDB ta bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a.
Rahotanni na nuni da cewa, yaro ɗaya cikin kowane yara 20 ne akale yi wa allurar rigakafi cikakke a Jihar Sakkwato a, a yayin da adadin mutuwar jarirai ya kai 104 daga cikin 1,000 a Jihar.
Ƙasa da kashi 14 cikin 100 na cibiyoyin lafiya a jihar ne suke da kayan aiki masu aiki, kuma likita ɗaya ne kawai ke kula da mutum 8,285, wanda ya gaza abin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayar na likita 1 ga 1,000 mutum.
Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPPKuɗaɗen da bankin ya ware za su tallafa wa samar kayan aikin kula da lafiya masu inganci a matakai uku na kula da lafiya a Jihar Sakkwato.
Wannan ya haɗa da gina sabon asibitin koyarwa mai gado 1,000, da manyan asibitoci na yankuna uku masu jimillar gadaje 450, da kuma cibiyoyin kiwon lafiya guda shida da aka tsara a domin kuka da al’ummomin karkara.
Aikin ya kuma haɗa da gyaran cibiyoyin horar da ma’aikatan lafiya da ƙirƙirar sabon ma’ajiyar magunguna ta zamani.
Darakta-Janar na Ofishin AfDB a Najeriya, Abdul Kamara, ya ce, “Wannan rancen na nuna yadda muke jajircewa wajen aiki tare da gwamnati don magance giɓin kayan kiwon lafiya a Najeriya, tare da gina cibiyoyin kula da lafiya masu ƙarfi da suka dace da tsari na yanayi.
“Ta hanyar ƙarfafa kayan aikin lafiya a Jihar Sakkwato, muna gina fata da hanyoyin samun kyakkyawan sakamako ga miliyoyin ’yan Najeriya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kiwon Lafiya lafiya Sakkwato a Jihar Sakkwato kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
Gwamnatin jihar Kwara ta kori mabarata 94 daga titunan Ilorin, domin tantancewa, gurfanar da su da kuma mayar da su gida.
Da take magana da ‘yan jarida yayin aikin, kwamishiniyar jin dadin jama’a da ci gaban jihar Dr Mariam Nnafatima Imam ta ce wadanda aka kama domin dawo da su sun hada da mata 43 da maza 51.
Ta ce ma’aikatar ta yi aikin dawo da mabaratan domin an haramta barace-barace a jihar Kwara.
Imam ya godewa gwamnan jihar bisa kokarin da yake yi na ganin jihar ta kawar da barace-barace a kan tituna da sauran matsalolin zamantakewa .
Kwamishinan ta ce a ko da yaushe gwamnatin jihar tana tuntubar gwamnatocin jihohin masu bara a tituna kafin a mayar da su jihohinsu.
A nasa jawabin, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan sha da fataucin miyagun kwayoyi, Haliru Mikail ya ce galibin mutanen da ke bayyana kansu a matsayin mabarata suna safarar kwayoyi.
Ya ce aikin dakile barace-barace a kan tituna zai ci gaba da kasancewa domin tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.
A nasa bangaren, shugaban sashin da ba na kariya ba, rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kwara Mista Adebayo Okunola ya bayyana cewa, an gudanar da aikin ne domin tsaftace jihar daga matsalolin zamantakewa yayin da wadanda aka kama tare da gurfanar da su a gaban kotun da ta dace za a hukunta su daidai da dokar jihar ta 2019.
Ya yi nuni da cewa hukumar da ke aikin za ta tabbatar da hukunta wadanda aka kama.
An gudanar da aikin ne a wasu yankuna da aka zaba a cikin birnin Ilorin da suka hada da Geri Alimi, Junction Tanke, Garage Offa, Garage Tipper da Zango, da dai sauransu.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU