2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Published: 2nd, August 2025 GMT
A yanzu haka dai ratotannin sun tabbatar da cewa APC da ADC suna gogayya wajen neman samun goyon bayan mutanen arewa kafin babban zaɓen 2027 ya ƙariso.
A ranar 1 ga Yuli, manyan ƴan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da dan takarar shugaban ƙasa a APC a 2023, Rotimi Amaechi, da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun gabatar da ADC a matsayin hadakar jam’iyyar adawa domin ƙalubalantar Tinubu a 2027.
Shugabannin ADC sun ci gaba da yin ƙoƙari don samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da sauran yankuna tun bayan buɗe jam’iyyar.
A taron, Mark ya buƙaci shugabannin arewacin Nijeriya da su daina dabi’ar zargi da kuma amincewa na suna da alhakkin ƙalubalen da yankin ke fuskanta.
Ya ce, “Wannan wata dama ce da kuma girmamawa kasancewa a gabanku yau don magana kan batun halin da muke ciki a yanzu da kuma sauya makomarmu. Ina kira a gare ku mu yi gaggawar samun haɗin kai da ƙarfafa dangantaka a matsayin hanyar magance ƙalubalen da yankinmu ke fuskanta.
“Arewacin da muka sani ya kasance wata ƙasa ce mai ɗimbin tarihi da albarkatun ma’adinai da ƙasa noma da al’adu masu yawa da kuma ƙarfin tasiri.
“ɗuk da wadannan albarkatu, muna fuskantar ƙalubale masu yawa da suka hada da rashin tsaro da talauci da rikice-rikicen ƙabilanci da addinai da rarrabuwar kai a siyasa da matsalolin zamantakewar da na tattalin arziki. Wadannan ƙalubale ba su faru a dare daya ba kuma ba za su kau ba har sai mun hada kai wajen daukar matakin da ya dace.
“ɗole ne mu yarda da cewa mu ne masu gina matsalolinmu, dole ne mu daina zargin kawunanmu idan muna son samun mafita ɗorewar yankinmu.”
Tsohon shugaban majalisar dattawa ya ƙara bayyana cewa rarrabuwar kawuna ta hana wa arewacin ƙasar nan ci gaba, yayin da halin ko-in-kula da rashin daukan mataki ya ƙara zurfafa rarrabuwar da ta riga ta wanzu.
“ƙalubalen da ke fuskantar arewacin Nijeriya suna da alaƙa da juna. Rashin tsaro yana janyo ficewar masu zuba jari, wanda hakan ke ƙara tsananta talauci. Talauci yana jawo aikata muyagun laifuka. ƙabilanci na rage ƙarfin haɗin kanmu wajen neman kyakkyawan shugabanci. Rugujewar harkokin siyasa na tabbatar da cewa ba za a samu ingantaccen ci gaba a yankinmu. Wannan ba arewar da muka gada ba ne,” in ji ADC.
ɗon dawo da martaban yanki, Mark ya jaddada cewa akwai buƙatar matanen arewa su sake tunani da yin Nazari wajen daukan matakan da suka dace.
Ya kira ga dukkan mutanen arewa su dauki wannan a matsayin babban nauyi na haɓaka haɗin kai wajen inganta yankin maimakon zama a rarrabe.
A nasa ɓangaren, Lawal ya bayyana cewa gamayyyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta arewa ta amince da ADC a matsayin jam’iyyar da ta iya tunkarar APC a zaɓen 2027.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya ya ce wakilai daga dukkanin jihohin arewa 19 sun cimma yarjejeniya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba ta wani yuƙuri wajen magance matsalolin yankin.
Ya ce masu ruwa da tsaki daga arewacin ƙasar nan sun amince su tashi tsaye su yada saƙonsu wajen samn haɗin kan mutane da cimma matsaya kan zaɓe mai zuwa.
A martaninsa, daraktan yada labarai na APC ya ce jam’iyyar mai mulki ba ta damu da abin da ake kira da suna hadakar jam’iyya ba.
Ibrahim ya bayyana cewa Shugaba Tinubu na jagorantar gwamnati mai cike da samun goyon bayan dukkan mutanen Nijeriya.
Ya ce, “Jam’iyarmu ta APC, tana samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da kuma dukkan sauyan yankunan Nijeriya gaba daya, sai dai wadanda ba su gamsu ba da suka kafa jam’iyyar ADC a yanzu.”
Ya bayyana cewa APC ta jajirce wajen sabunta fata ga ƴan Nijeriya kuma yana nuna tabbacin cewa jam’iyyar za ta ƙara samun nasara a 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Arewa samun goyon bayan mutanen arewa arewacin Nijeriya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
Firaminista Mark Carney ya ce Canada ta shirya amincewa da kafa ƙasar Falasɗinu a cikin watan Satumba, inda ta zamo ƙasa ta uku daga cikin ƙungiyar G7 da ta fitar da irin wannan sanarwa a cikin kwanakin nan.
Carney ya ce za su ɗauki matakin ne ta la’akari da wasu sharuɗɗan gyara daga ɓangaren hukumomin Falasɗinu da suka haɗa da amincewa da tsarin dimokuraɗiyya da kuma gudanar da zaɓe ba tare da ƙungiyar Hamas ba a shekara mai zuwa.
Sanarwar tasa na zuwa ne kwana ɗaya bayan Birtaniya ta bayyana goyon bayan ta ga kafa ƙasar Falasɗinun a watan Satumba mai zuwa, kuma mako ɗaya bayan Faransa ta yi irin wannan sanarwa.
Ma’aikatar harkokin wajen Isra’ila ta yi watsi da sanarwar ta Canada tana mai cewa matakin tamkar jinjinawa ƙungiyar Hamas ne.
Daga cikin ƙasashe 193 na Majalisar Dinkin Duniya, 147 sun goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu.
Amma Mr Carney ya ce Canada za ta goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinun ne a babban taron Majalisar Dinkin Duniya mai zuwa.
Ya kafa hujja da yadda Isra’ila ke ƙara mamaye sassan gaɓar yamma da kogin Jordan da taɓarɓarewar ayyukan jin ƙai a Gaza da kuma harin da Hamas ta kai wa Isra’ila a ranar bakwai ga watan Oktoba a matsayin dalilan da suka sa Canada ta sauya matsayarta a kan batun.
Carney ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba cewa “Mawuyacin halin da ake ciki a Gaza na ƙara taɓarɓarewa,”
Ya ce kafa ƙasar Falasɗinu zai bai wa jagororin Falasɗinawa damar gudanar da tsare-tsaren mulki da gudanar da zaɓuka ba tare da Hamas ba a 2026 da kuma kawo ƙarshen ayyukan ƙungiyoyi masu riƙe da makamai a yankin.
Dama can Canada ta daɗe tana goyon bayan shirin kafa ƙasashe biyu masu ƴancin kansu a matsayin hanyar warware rikicin Falasɗinawa da Isra’ila.
Carney ya kuma ce ya tattauna da shugaban Falasɗinawa Mahmud Abbas a kan batun.
Hukumomin Falaɗinawa dai suna iko da wasu sassa na gaɓar yamma da kogin Jordan a ƙarƙashin jam’iyyar Fatah da shugaba Abbas ke jagoranta, yayin da ƙungiyar Hamas ke tafiyar da Gaza. Dukkan su ba su taɓa gudanar da zaɓe ba tun a 2006.
Firaminitan Canada ya fuskanci matsin lambar neman ya sanar da matsayar sa kan kafa ƙasar Falasɗinu tun bayan da manyan ƙawayen ƙasarsa, Birtaniya da Faransa suka sanar da goyon bayan su.
Jakadun Canada da jami’an diflomasiyyarta fiye da 200 suka sanya hannu kan wata takarda mai neman Carney ya amince da shirin
A cikin wasiƙar da suka aikewa Carney jami’an sun ce yaƙin da Isra’ila ke yi a Gaza ya yi hannun riga da tsarin ƙasar.
Da aka tambaye shi ko Canada ta goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinun ne saboda Birtaniya ta janye hankalin ta, sai Mr Carney ya ce ƙasarsa ta ɗauki matakin ne ba tare da katsalandan daga wata ƙasa ba.
Carney ya jaddada cewa Canada ƙasa ce mai ƴancin kanta kuma wadda ke da ikon tsara yadda za ta yi alaƙa da ƙasashen duniya.
Da wannan mataki dai ana iya cewa Canada ta bi turbar da sauran ƙawayenta na Turai suka bi game da kafa ƙasar Falasɗinu.
Idan Birtaniya da Faransa suka jaddada goyon bayansu ga kafuwar ƙasar Falasɗinu, zai rage saura Amiurka ce kaɗai ke adawa da hakan a cikin ƙasashe mambobin dindindin a kwamitin taro na Majalisar Dinkin Duniya.
Ma’aikatar lafiya ta Hamas ta ce mutane aƙalla 60,034 aka kashe a Gaza tun bayan fara yaƙi a Gaza, kuma ta ce aƙalla 1,200 daga cikin su sun mutu ne saboda rashin abinci mai gina jiki, yayin da 89 a cikin su ƙananan yara ne.
BBC/Hausa