Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Published: 2nd, August 2025 GMT
Bayan shekar 22 da kuɓutar da Nijeriya daga mulkin soja, dimokuraɗiyya na ci gaba da fama da rauni mai tsanani. Alamun cutar sun bayyana ne a cinikin baragurbin wakilai (delegates), amfani da kuɗin ƙasa da aka wawure ta hanyar haram wajen gudanar da yaƙin neman zaɓe, maƙudan kuɗin da ake ware wa Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC), ƙarancin yawan masu kada ƙuri’a, sayen ƙuri’u a bainar jama’a, tashin hankali yayin zaɓe, da kuma yaɗuwar fargaba, musamman a tsakanin matasa, cin amana na ƴan siyasa, canja sheƙa da zaɓaɓɓu ke yi, da dai sauran makamantansu.
Asalin matsalar ita ce, rashin shiga cikin gudanar da gwamnati a siyasance (eɗclusion) na masu gaskiya da riƙon amana, matasa, mata, masu fama da naƙasa, ƴan gudun hijira da jam’iyyun da ke da ƙaramin ƙarfi, duk sun kasance a wajen filin.
Wannan ba kawai rashin adalci ba ne, har ma ya saɓa wa kundin tsarin mulki, kuma barazana ce ga zaman lafiya da ci gaban ƙasa. Idan ka duba, za ka fahimci cewa; dimokuraɗiyyarmu na hannun wasu tsirarun mutane da shugabannin jam’iyyu masu ƙarfi, wadanda suka killace matasa da sauran ƴan Nijeriya daga samun damar shiga siyasa ko a saurare su ko la’akari da tasu gudunmawar. ɗimokuraɗiyyar cikin gida a jam’iyyu, abin dariya ne kawai, domin an mayar da zaɓe na cikin gida zuwa ciniki, wato ba ni kuɗi ga ƙuri’a. Inda a wani ɓangaren kuma, INEC na fuskantar ƙalubalen rashin ƴanci da rashin ƙwarin guiwar aiwatar da dokokinta.
Har ila yau, ƴan gudun hijira da sauran al’umma masu rinjaye ana ci gaba da ware su daga zaɓe. Haka nan, hukumar zaɓen jihohi, musamman yadda aka gani a zaɓen ƙananan hukumomi a Kaduna da Bauchi, sun zama wani kwafi da ya ci mutuncin dimokuraɗiyya. Wannan ya saɓa wa sassa da dama na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (Sashe 14(2)(a), 15(1), 40, 153(1)(f), 221, 318(1), da Jadawali na Bakwai), da ɗokokin ƙungiyar Tarayyar Afirka da kuma Majalisar ɗinkin ɗuniya.
Yadda Wannan Tsari Na Matasa Zai Taimaka Wajen Ceto Siyasarmu:
1-Yarjejeniya Ta ƙasa ɗon Siyasa Mai Inganci (National Charter for Inclusion): A samar da wata Yarjejeniya ta haɗin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Matasa ta ƙasa, ƙungiyar Gamayyan Jamíyyun Siyasa (IPAC), Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC), ƙungiyoyin Fararen Hula da Majalisar Matasa ta Nijeriya. Wannan yarjejeniya za ta kafa ƙa’idoji da dokokin da za su tilasta dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyu, tabbatar da adalci wajen zaɓuɓɓuka da kuma bai wa dukkannin jam’iyyun da suka shiga zaɓe damar ba da gudunmuwa wajen shugabanci a kowane mataki da kuma bai wa matasa, mata, ƴan gudun hijira da kowa da kowa damar ƴancin tsayawa takara cikin adalci.
2- Sauyi Mai Zurfi Ga Jam’iyyu da Tsarin Zaɓe:
Ya zama wajibi jam’iyyu su buɗe ƙofa. A kafa dokar da za ta tilasta duk mai son tsayawa takara gabatar da “Tsarin Ayyuka” (Project Plans) kafin hawa kujera, sannan ya fitar da “Rahoton ƙarshe” (End-of-Term Reports), bayan barin gado ko da kuwa zai koma kuwa. A daƙile kuɗin da ake nema marasa tushe daga masu neman takara, musamman na hukumomin zaɓen jihohi, (Misalin KAɗ-SIECOM). A tabbatar da cikakken amfani da Sashe na 7 na Kundin Tsarin Mulki da ɗokar Zaɓe ta 2022.
3- Runguman ɗimokuraɗiyyar ɗijital Hannu Biyu (ɗigital ɗemocracy):
A kafa “Cibiyar ɗimokuraɗiyyar ɗijital ta ƙasa (NɗɗH)” da za ta sa ido, bayar da rahoto kai tsaye, sa ido kan kuɗin yaƙin neman zaɓe da tantance tsarin jam’iyyu. Za ta kuma ba da damar samun ilimin siyasa ta hanyar wasanni da fasahar zamani domin ƙara fahimta, rage rashin sha’awa daga matasa, da bunƙasa ilimi da riƙon amana.
4- Ƙarfafa IPAC Youth da Shirye-shiryen Fadakarwa:
A ƙarfafa ɓangaren Matasa na IPAC (IPAC Youth ɗirectorate) daga matakin ƙasa har zuwa jihohi, ta hanyar samar da doka, kasafin kuɗi da kuma tsarin aiki. Sannan, a ɗora musu alhakin wayar da kan jama’a a faɗin ƙasar nan, musamman a tsakanin wadanda aka ware daga siyasa.
Me Za Mu Samu Idan An Bi Wannan Hanya? Za mu samu dimokuraɗiyya mai inganci da kuma tsabta, inda matasa, mata, masu fama da nakasa (PWɗs) da ƴan gudun hijira (IɗPs) za su samu bakin fada kuma a ji a cikin siyasa da shugabanci. Za a samu ƙarancin tashin hankali a lokacin zaɓe, raguwar sayen ƙuri’a da ingantaccen ilimi da wayewa a tsakanin jama’a. Za kuma a samu jam’iyyu masu gaskiya da amana da kuma shugabanci na ƙwarai da ci gaban ƙasarmu Nijeriya.
Matakan Aiwanar da Wannan Tsari:
Mataki na 1:
Rubuta NSPPC tare da dukkan masu ruwa da tsaki.
Mataki na 2: Kafa tsarin dubawa tsakanin INEC, IPAC da CSO.
Mataki na 3: ƙaddamar da NɗɗH da kayan aikin ilmantarwa.
Mataki na 4: Gyaran ɗokar Zaɓe, domin shigar da wadanan al‘amura da muka gabatar a sama da sauran buƙatu.
Kafin Mu Kammala: Makomar dimokuraɗiyyar Nijeriya na cikin hadari. Ba za mu iya ci gaba da kallon halin da ake ciki ba na rashin adalci, cin amana, zangon ƙasa ga ƙasa da al’úmarta.
Yazama wajibi mu yi amfani da ƙarfin matasa, domin ceto Nijeriya daga bakin kuraye. ƙirƙire-ƙirƙire da buƙatar riƙon amana, su ne maganin cutar da dimokuraɗiyyarmu ke fama da ita.
Wannan tsari nawa na zuwa ne daga gwanancewa da aiki da IPAC, shirye-shiyen fitar da saƙwanni ta ‘Bakondare Speaks’, wallafa rubuce-rubuce a manyan jaridu kamar su Premium Times, daily Trust, Guardian, Punch, Vanguard, Thisday , Leadership (A hausance da turanci)) da kuma shiga ayyukan siyasa masu tsafta da kuma alaƙa da ƙungiyoyi masu muhimmanci na siyasa.
Yanzu ne lokacin sauyi! Muryar matasa ya kamata ta koma tsakiya wajen tsara manufofi da aiwatar da su. Yakamata dimokuraɗiyyar Nijeriya ta amfani kowa da kowa ba wasu ba kawai!
Kafin rahoton ƙarshe na wannan taro ya isa ofishin Shugaban ƙasa ranar 12 ga Agusta, 2025 (Ranar Matasa ta ɗuniya), ina kira da babbar murya da fatan alheri ga duk dan Nijeriya da kuma dukkan wakilai da su rungumi wannan tsari. Ina kuma kira ga ƴan majalisa da masu zartarwa da su aiwatar da shi, domin ci gaban Nijeriya da kuma amfanin masu zuwa nan gaba. Yanzu ne lokacin daukar mataki na haƙiƙa da Jarumta! Allah ya yi mana albarka, ameen.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: ƴan gudun hijira Nijeriya daga Nijeriya da
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta ce ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su, bayan sun yi artabu da wasu da ake zargin sun yi garkuwa da su a wani mummunan musayar wuta da aka yi a tsaunin Shanga.
Waɗanda aka yi garkuwan da su sun haɗa da: Muhammad Nasamu Namata mai shekara 25, da Gide Namata mai shekara 20 da Hamidu Alhaji Namani mai shekara 35.
INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a KebbiAn yin garkuwa da su ne a safiyar ranar 27 ga watan Yuli, 2025, lokacin da masu garkuwa da mutane ɗauke da makamai suka mamaye ƙauyen Sangara da ke Ƙaramar hukumar Shanga.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa wannan ceton ya biyo bayan ɗaukar matakin gaggawa da jami’an ’yan sanda na yankin Shanga suka ɗauka, wanda ya haɗa tawagar jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an sojojin Najeriya, jami’an tsaro na Civil Defence da ’yan banga na yankin da mafarauta.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ta bi sahun masu garkuwa da mutanen ne zuwa tsaunin Shanga, inda aka yi musayar wuta a tsakaninsu, musayar wutar ta sa jami’an tsaro suka yi nasara kan masu garkuwar.
Daga nan masu garkuwan suka tsere zuwa cikin daji da raunukan harbin bindiga.
“An kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su ne ba tare da wani rauni ba, a ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2025 da misalin ƙarfe 3:30 na rana kuma a halin yanzu suna samun kulawar likita kafin su sake haɗuwa da iyalansu.”
Ya ce, Kwamishinan ’yan sanda, CP Bello M. Sani ya yaba wa jarumtaka da ƙwarewa na rundunar, inda ya buƙaci dukkan hukumomin tsaro su ci gaba da haɗa kai. Ya nanata ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a Jihar Kebbi.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su sanya ido tare da kai rahoto ga jami’an tsaro mafi kusa domin ɗaukar matakin gaggawa.