Aminiya:
2025-10-14@14:49:42 GMT

’Yan Majalisar Tarayyar Kaduna 3 sun sauya sheka zuwa APC

Published: 14th, October 2025 GMT

’Yan Majalisar Tarayya uku daga Jihar Kaduna sun sauya sheka daga Jam’iyyar PDP zuwa APC.

Shugaban Majalisar Wakilai Abbas Tajuddeen ya sanar a ranar Talata cewa masu sauya shekar sun hada da Honorabul Abdulkarim Hussain Mohammed, Aliyu Mustapha Abdullahi da kuma Sadiq Ango Abdullahi.

Tajuddeen, wanda shi ma dan asalin Jihar Kaduna ne, ya sanar da cewa, Gwamnan jihar, Uba Sani ya halarci zaman majalisar domin shaida dawowar ’yan majalisar zuwa APC daga PDP.

Masu sauya shekar sun bayyana cewa rikin cikin gida da rabuwar kai da suka dabaibaye tsohuwar jam’iyyarsu ta PDP ce ta sa suka yanke shawarar sauya sheka.

Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila

Jim kadan bayan sanar da sauya shekar tasu ce Gwamna Uba Sani ya jagorance su zuwa ga shugaban majalisar inda suka dauki hoto kafin shi da tawagarsa su wuce.

Tuni dai Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar Wakilai, Kingsley Chinda, ya kalubalanci sauya shekar, yana mai kira ga shugaban majalisar da ya kwace kujerunsu, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: sauya sheka sauya shekar

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

A cewar su, wannan sabon tsarin zai taimaka wajen gina dimokuraɗiyya mai ƙarfi da ɗorewa a ƙasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ilimi Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba October 13, 2025 Manyan Labarai Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano October 13, 2025 Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Juyin mulki: Shugaba Rajeolina ya tsere daga ya rushe majalisa
  • Cirar kudin kwastoma: Majalisa ta gayyaci CBN da bankuna
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • Rasha ta kai wa tawagar kayan agajin MDD hari a Ukraine
  • Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna