’Yan Majalisar Tarayyar Kaduna 3 sun sauya sheka zuwa APC
Published: 14th, October 2025 GMT
’Yan Majalisar Tarayya uku daga Jihar Kaduna sun sauya sheka daga Jam’iyyar PDP zuwa APC.
Shugaban Majalisar Wakilai Abbas Tajuddeen ya sanar a ranar Talata cewa masu sauya shekar sun hada da Honorabul Abdulkarim Hussain Mohammed, Aliyu Mustapha Abdullahi da kuma Sadiq Ango Abdullahi.
Tajuddeen, wanda shi ma dan asalin Jihar Kaduna ne, ya sanar da cewa, Gwamnan jihar, Uba Sani ya halarci zaman majalisar domin shaida dawowar ’yan majalisar zuwa APC daga PDP.
Masu sauya shekar sun bayyana cewa rikin cikin gida da rabuwar kai da suka dabaibaye tsohuwar jam’iyyarsu ta PDP ce ta sa suka yanke shawarar sauya sheka.
Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ilaJim kadan bayan sanar da sauya shekar tasu ce Gwamna Uba Sani ya jagorance su zuwa ga shugaban majalisar inda suka dauki hoto kafin shi da tawagarsa su wuce.
Tuni dai Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar Wakilai, Kingsley Chinda, ya kalubalanci sauya shekar, yana mai kira ga shugaban majalisar da ya kwace kujerunsu, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: sauya sheka sauya shekar
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026
A cewar su, wannan sabon tsarin zai taimaka wajen gina dimokuraɗiyya mai ƙarfi da ɗorewa a ƙasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA