Aminiya:
2025-11-28@11:33:11 GMT

Sakin Maryam Sanda shi ne ƙololuwar zalunci —Dangin Bilyaminu

Published: 14th, October 2025 GMT

Dangin Marigayi Bilyaminu Ahmed Bello sun bayyana takaicinsu bisa sanya matarsa, Maryam Sanda, wadda kotu ta ɗaure ta kan laifin soka masa wuka har lahira, a cikin jerin mutanen da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa afuwa.

A shekarar 2020 ne kotu ta yanke wa Maryam Sanda hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun ta da laifin kashe mijinta Bilyaminu.

Sanarwar da dangin marigayin suka fitar ɗauke da sa hannun Dakta Bello Haliru Mohammed (Dangaladiman Gwandu) ta bayyana afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda a matsayin “mummunan famu,” da kuma ƙololuwar rashin adalci ga ɗan uwansu.

Sun bayyana takaici bisa sakin Maryam Sanda daga gidan yari, wanda suka kira da neman faranta wa danginta rai, ba tare da la’akari da rabi na har abada da ta yi wa ’yan uwa da iyaye da dangi da a aminan Bilyaminu da kashe ba.

Maryam Sanda mai shekara 37 tana daga cikin jerin mutane 175 da Shugaba ya yi wa afuwa a ranar Alhamis da ta gabata.

Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawa

Laifukan da aka yanke musu hukunci su haɗa da cin amanar ƙasa, kisan kai, da masu sayar da makamai ga ’yan ta’adda da masu garkuwa da mutane da dillalan  miyagun ƙwayoyi da ’yan damfara da masu haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

Sanarwar da kakakin Shugaban Ƙasa Bayo Onanuga ya fitar ta nuna cikinsu akwai masu zaman rai da rai da aka yi wa afuwa gaba ɗaya da waɗanda aka sassauta hukuncin.

Akwai kuma wadanda aka yi wa afuwa bayan ransu kamar Manjo-Janar Mamman Vatsa da Cin Herbert Macaulay da Ken Saro Wiwa, da fitattun mutane irin su Farfesa Wole Soyinka da Faruk Lawan da Farfesa Magaji Garba da Manjo Akubo da sauransu.

Jerin sunayen mutanen da aka yi afuwar ya haifar da ce-ce-ku-ce. Onanuga ya ce an yi musu afuwa ne bayan sun nuna nadama tare da zama mutanen kirki gami da yawan shekaru da sauransu.

Shari’ar Maryam Sanda

Dambarwar Maryam Sanda yana daga cikin shari’o’in rikicin ma’aurata da ya kai ga kisa suka fi ɗaukar hankali a baya-bayan nan.

Abin ya faro ne bayan rikici tsakaninta da Bilyaminu wanda a ƙarshe ta soka masa wuƙa har lahira.

Ta musanta tuhumar da ake mata, a ayin da aka gurfanar da ita a gaban Babbar Kotun Abuja.

Bayan tsawon lokaci ana shari’a, a watan Disambar 2020, Mai Shari’a Yusuf Halilu, na Kotun Ɗaukaka Ƙara yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, wanda daga baya Kotun Koli ta tabbatar a watan Oktoba 2023.

Daga lokacin zuwa yanzu ta yi zaman shekara shida da wata takwas a Babban Gidan Yarin Suleja.

Martanin dangin Bilyaminu

Dangin Bilyaminu sun bayyana sakin Maryam Sanda a matsayin “rashin adalci mafi raɗaɗi da za a iya jefa iyali saboda wanda suke ƙauna,” inda suka bayyana ta a matsayin “mai kisa da kotu ta tabbatar da laifinta” wadda ba ta taɓa nuna nadama ba tun daga farkon shari’arta har zuwa ƙarar da ta daukaka.

Sun ce tun bayan mummunan abin da ya faru a ranar 19 ga Nuwamba, 2017, sun zabi su yi shiru saboda girmama ’ya’yan da aka bari, duk da ƙaryar ɓangarenta ake yaɗawa.

Sun bayyana cewa sun dogara ne da tsarin shari’a, wanda ya tabbatar da hukuncin kisa da kotunan farko suka yanke — har zuwa Kotun Koli a 2023.

Iyalin sun ce wannan hukunci ya ba su ɗan nutsuwa, amma yafiyar shugaban ƙasa ta sake buɗe musu raunin da ke ci gaba da zubar da jini, tare da rage darajar rayuwar wanda aka kashe. Sun soki dalilan yafiyar, suna cewa an yi ta ne bisa roƙon iyalan Sanda, alhali kuwa Bilyaminu ma ɗa ne, aboki, kuma uba mai ƙauna wanda “aka tauye masa damar rayuwa da renon ’ya’yansa.”

Sun kammala da cewa sun bar komai ga adalcin Allah, “Mai Shari’a na gaskiya,” tare da yin addu’a ga Allah Ya jikan Bilyaminu, Ya kuma ba ’ya’yansa da masoyansa ƙarfin jure wannan raɗaɗin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Bilyaminu Maryam Sanda Yafiya Maryam Sanda sun bayyana Sun bayyana yi wa afuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ce Najeriya na iya ajiye biliyoyin naira a duk shekara idan aka rungumi tsarin majalisa ta wucin gadi.

Yayin da yake magana a gidan talabijin na Channels ranar Alhamis, Ndume ya ce kuɗin da ake kashewa wajen kula da Majalisar Dokoki a tsarin zama kodayaushe ba zai dore ba, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke fama da matsalolin kuɗi da tsaro.

An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra

“Kudin gudanar da gwamnati ya yi yawa sosai. Idan ’yan majalisa suka zauna na wucin gadi, gwamnati za ta ajiye biliyoyi,” in ji shi.

Ya ce za a iya sauya akalar kuɗin zuwa bangaren tsaro da sauran muhimman abubuwan ƙasa.

Ndume ya danganta tsadar gudanar da gwamnati da manyan ƙalubale da ke hana ƙasar yin nasara wajen yaki da rashin tsaro.

Ya ce Najeriya ba za ta iya jure ɓarnar kashe kuɗi ba a yayin da ake fuskantar ta’addanci a Arewa maso Gabas, ’yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, garkuwa da mutane, da kuma ƙaruwar laifuka.

A wani bangare na fafutukar rage kashe kuɗi, sanatan ya soki ci gaba da kasancewar ’yan sanda da ke tare da sanataci da sauran manyan mutane duk da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an tsaro daga irin wannan aiki.

Aminiya ta rawaito cewa Shugaban Ƙasa ya umarci Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da ya janye jami’an daga aikin kare manyan mutane ya kuma tura su zuwa fagen yaki da ta’addanci da samar da tsaro.

“Amma har yanzu, ’yan siyasa na tare da ’yan sanda,” in ji Ndume, yana kira ga Babban Sufeton da ya tabbatar da cikakken bin umarnin na shugaban ƙasa.

Ya bayyana cewa tura ’yan sanda daga aikin kare manyan mutane zuwa aikin al’umma da na fagen yaki zai ƙara inganta tsaron ƙasa fiye da ɗaure su ga mutum ɗaya.

Ndume ya ce tsarin tsaron ƙasa ya yi ƙunci kuma yana bukatar “haɗa hannaye wajen yin aiki,” yana mai jaddada cewa dubban jami’an suna makale wajen rakiyar ’yan siyasa da masu tasiri waɗanda za su iya rayuwa ba tare da irin wannan rakiyar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamɓararren Shugaban Guinea-Bissau ya gudu Senegal
  • Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna