Shugaban Ƙungiyar Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Alhaji Ibrahim Ahmad Jikamshi, zai jagoranci wata tawaga ta musamman domin ganawa da Babban Sakataren Hukumar PTAD kan muhimman batutuwa fansho da ta shafi tsofaffin ma’aikatan.

Alhaji Ibrahim Jikamshi dayake bayani a Kaduna, yace za a gudanar da wannan ganawa a cikin wannan mako domin tattaunawa kan wasu matsaloli da aka gano wajen biyan bashin da ake bin tsofaffin ma’aikatan shekaru da dama.

Ya tabbatar da cewa ƙungiyar tana ƙoƙari wajen shawo kan irin waɗannan matsaloli da suka dade ana fama da su, tare da fatan cewa hukumar PTAD za ta nuna gaskiya, rikon amana da kuma jajircewa wajen biyan hakkokin da suka rage.

Alhaji Ibrahim Jikamshi, wanda ya tunatar da matakin da shugaban ƙasa ya ɗauka a baya na biyan bashin da ake bin tsofaffin ma’aikata ta hanyar sakin biliyoyin Naira, ya nuna damuwa da cewa har yanzu wannan mataki bai haifar da gamsasshen sakamako ba ga waɗanda abin ya shafa.

SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100

Kwamitin da ke kula da tsare-tsare da manufofin kuɗi na Babban Bankin Najeriya (CBN) ya zaftare maki 60 daga nauyin kuɗin ruwa da ke kan masu karɓar basussuka. 

Wannan dai shi ne karo na farko cikin shekaru biyar da aka samu babban bankin ya yi rangwamin kuɗin ruwa a ƙasar.

CBN ɗin ya ce kwamitin a wannan Talatar ya rage yawan kuɗin ruwan daga kashi 27.5 da yake karɓa a baya zuwa kashi 27 a yanzu.

Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a Taraba An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

Gwamnan Babban Bankin, Olayemi Cardoso, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai bayan kammala taron kwamitin karo na 302 da ya gudana a Abuja.

Cardoso, ya bayyana cewa an kuma mayar da buƙatar adana tsabar kuɗi a manyan bankuna zuwa kashi 45 cikin ɗari, yayin da na bankunan ’yan kasuwa aka bar shi a kashi 16 cikin ɗari.

Haka kuma, Babban Bankin ya ƙaddamar da matakin sanya kashi 75 cikin ɗari na tsabar kuɗin da aka adana mallakin ma’aikatu da hukumomin gwamnati da ba sa cikin asusun gwamnati na bai-ɗaya wato TSA.

Cardoso ya bayyana cewa wannan mataki na kwamitin na zuwa ne bayan sauƙin da aka fara gani a farashin kayayyakin a ’yan kwanakin nan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yada labaran karya a intanet babban laifi ne a Musulunci – Sheikh Ibrahim Khalil
  • Yarima Salman ya jagoranci jana’izar babban mai ba da fatawa na Saudiyya
  • CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100
  • Majalisa ta ɗage ranar dawowarta zuwa 7 ga watan Oktoba
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Sarkin Ruman Katsina ya rasu
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi                         
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe