Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
Published: 15th, April 2025 GMT
Rahoton Kungiyar Kasashe Masu Samar da Man Fetur (OPEC) ya nuna cewa Nijeriya ta ci gaba da riƙe matsayinta na ƙasa mafi yawan samar da ɗanyen man a nahiyar Afirka a watan Maris.
OPEC ta ce hakan ya faru ne duk da raguwar yawan man da ƙasar ta samar a watan da ya gabata.
Sabon rahotonta na wata-wata da ta fitar a ranar Litinin ya ce yawan man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga miliyan 1.
A cewar rahoton, duk da raguwar, yawan man da Nijeriya ta samar shi ne mafi yawa a Afirka, inda ya zarce Algeria da Congo.
An yi garkuwa da masu ibada a Kogi Noman rake: Najeriya da China sun kulla yarjejeniyar kasuwancin $1bn Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a GazaOPEC ta kara da cewa ta hanyar ci gaba da ƙarfin da ta samu a watan Fabrairu, Nijeriya ta zarce Algeria, wacce ta samar da ganga 909,000 a kowace rana, da kuma Congo, wacce ta samar da ganga 263,000 a kowace rana.
Ta ci gaba da da cewa Nijeriya ta samar da ganga miliyan 1.51 a kowace rana a watan Maris, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.54 a kowace rana a watan Fabrairu.
Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Sama ta Nijeriya (NUPRC) ta ce yawan man da ƙasar ta samar ya ragu zuwa ganga 1,400,783 a kowace rana a watan Maris.
Duk da raguwar yawan man da aka samar a watan Maris, NUPRC ta ce matsakaicin yawan ɗanyen man da aka samar ya kai kashi 93 cikin ɗari na adadin ganga miliyan 1.5 da OPEC ta ware wa Nijeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya a kowace rana a watan ganga miliyan 1 a watan Maris yawan man da Nijeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya halarci taron mataki na 2 da na 3 na ganawar shugabannin BRICS karo na 17 da aka gudanar a Rio de Janeiro hedkwatar kasar Brazil, tsakanin ranakun 6 zuwa 7 ga watan nan da muke ciki, tare da gabatar da jawabi.
Li ya ce, hadin gwiwar kasashen BRICS dole ne ya nace ga matsayin kiyayewa da tabbatar da cudanyar bangarori daban-daban a duniya, da gaggauta kafa tsarin ciniki da tattalin arzikin duniya mai adalci da bude kofa, da hada kan kasashe masu tasowa, don taka rawar gani ga samun bunkasar duniya mai dorewa.
Ya kara da cewa, ya kamata a dukufa kan shimfida halayen tattalin arzikin duniya mai bude kofa, da daga matsayin hadin gwiwar kasa da kasa kan harkar hada-hadar kudi, da ma bullo da wata sabuwar hanyar samun bunkasar tattalin arziki. A nata bangare, Sin za ta samar da abun koyi dangane da hadin gwiwar yanar gizo tsakanin kasashe masu tasowa karkashin shawarar raya duniya, don gabatar da ayyukan ba da horo har 200 ga kasashe masu tasowa a shekaru 5 da suke tafe, a bangaren tattalin arzikin yanar gizo, da fasahar AI da sauransu.
Li ya kuma jadadda cewa, dole ne al’ummun duniya su hada hannunsu wajen tinkarar sauyin yanayi, da kara samun ingantaccen ci gaban kiyayen muhallin hallitu, da gaggauta karfin gudanar da ayyukan kiwon lafiyar jama’a. Kuma Sin za ta ci gaba da daukar nagartattun matakai, da sauke nauyin dake wuyanta, na kokarin ciyar da hadin gwiwar mabambantan bangarori don samun bunkasa mai kiyaye muhalli a dogon lokaci. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp