Rahoton Kungiyar Kasashe Masu Samar da Man Fetur (OPEC) ya nuna cewa Nijeriya ta ci gaba da riƙe matsayinta na ƙasa mafi yawan samar da ɗanyen man a nahiyar Afirka a watan Maris.

OPEC ta ce hakan ya faru ne duk da raguwar yawan man da ƙasar ta samar a watan da ya gabata.

Sabon rahotonta na wata-wata da ta fitar a ranar Litinin ya ce yawan man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga miliyan 1.

40 a kowace rana a watan Maris, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.46 a kowace rana a watan Fabrairu.

A cewar rahoton, duk da raguwar, yawan man da Nijeriya ta samar shi ne mafi yawa a Afirka, inda ya zarce Algeria da Congo.

An yi garkuwa da masu ibada a Kogi Noman rake: Najeriya da China sun kulla yarjejeniyar kasuwancin $1bn Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza

OPEC ta kara da cewa ta hanyar ci gaba da ƙarfin da ta samu a watan Fabrairu, Nijeriya ta zarce Algeria, wacce ta samar da ganga 909,000 a kowace rana, da kuma Congo, wacce ta samar da ganga 263,000 a kowace rana.

Ta ci gaba da da cewa Nijeriya ta samar da ganga miliyan 1.51 a kowace rana a watan Maris, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.54 a kowace rana a watan Fabrairu.

Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Sama ta Nijeriya (NUPRC) ta ce yawan man da ƙasar ta samar ya ragu zuwa ganga 1,400,783 a kowace rana a watan Maris.

Duk da raguwar yawan man da aka samar a watan Maris, NUPRC ta ce matsakaicin yawan ɗanyen man da aka samar ya kai kashi 93 cikin ɗari na adadin ganga miliyan 1.5 da OPEC ta ware wa Nijeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya a kowace rana a watan ganga miliyan 1 a watan Maris yawan man da Nijeriya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro

Gwamnatin Tarayyar Najeriya da Masarautar Saudiyya sun sanya hannu kan wata sabuwar yarjejeniya domin ƙarfafa dangantakar tsaro da haɗin gwiwar soja tsakanin ƙasashen biyu.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle kan yaɗa labarai Ahmed Dan Wudil ya fitar, ta bayyana cewa yarjejeniyar za ta shafi muhimman fannoni kamar musayar bayanan leƙen asiri, horas da sojoji, haɗin gwiwa a harkar samar da kayan yaki da kuma gudanar da ayyukan tsaro tare.

Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana

Minista Matawalle ne ya sanya hannu a madadin Najeriya, yayin da Dakta Khaleed H. Al-Biyari ya sanya hannu a madadin Gwamnatin Masarautar Saudiyya.

Ministar ya bayyana cewa, wannan ci gaban babbar dama ce da za ta ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu da kuma taimakawa wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da Najeriya ke fuskanta a halin yanzu.

Ya ce, ma’aikatar tsaron Najeriya tana maraba da wannan ci gaba, tare da fatan hakan zai taimaka wajen kawo ƙarshen matsalolin tsaro da ake fama da su a sassa daban-daban na ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro