Domin tabbatar da bin bin doka da oda a tsakanin al’umma, ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi ta ce za ta fara wani gangamin wayar da kan jama’a na tsawon mako takwas.

 

A cewar kwamishinan, gangamin zai mayar da hankali ne wajen wayar da al’umma, masana’antu, da sauran masu ruwa da tsaki kan sabbin dokokin da kuma muhimmancin kiyaye muhalli mai tsafta.

 

Ya kuma sanar da cewa, za a fitar da dokokin a cikin harsunan Hausa da Ingilishi a cikin mako guda domin inganta yanayin fahimtar dokokin a tsakanin al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka

Gwamnatin Tarayya ta bayyana aniyar ta na hadin gwiwa da Cibiyar Binciken Cututtuka ta Jihar Kano(KIRCT) a fannonin bincike, samar da rigakafi, habaka magunguna da kuma yaki da cututtuka masu nasaba da zafi (tropical diseases).

Darakta Janar na Hukumar Binciken Harkokin Halittu ta Kasa (NBRDA), Farfesa Abdullahi Mustapha ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma da ya kai hedikwatar KIRCT  da ke Kano.

Farfesa Mustapha ya ce ziyarar na da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin NBRDA da KIRCT domin magance kalubalen da kasa ke fuskanta ta hanyar binciken zamani.

“A matsayina na shugaba a wata muhimmiyar hukuma da ke da alhakin bincike da ci gaban fasahar halittu a fannonin abinci da noma, lafiya, masana’antu da muhalli, muna da cikakken shiri na tallafa wa KIRCT don cimma manufofinta.”

Ya yaba da kayan aiki na zamani da ke cibiyar, yana mai cewa suna da babban amfani wajen kawo sakamako mai tasiri da kuma daga martabar Najeriya a fagen binciken kimiyya na duniya.

A nasa jawabin, Daraktan Janar na KIRCT, Farfesa Hamisu Salihu, ya bayyana cewa cibiyar na mai da hankali kan muhimman fannoni guda uku da suka hada da taimaka wa manyan masu bincike daga Jami’ar Bayero ta Kano da Jami’ar Northwest, da  horar da sabbin masana bincike, wato masu tasuwa, da kuma kaddamar da wani shirin gwaji na horas da dalibai biyar mafi hazaka daga ajin karshe na sakandare kan ilimin fasahar halittu kafin su shiga jami’a.

Farfesa Hamisu ya jaddada muhimmancin kafafen watsa labarai da kuma Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano wajen bunkasa fasahar halittu da inganta tattalin arzikin ilimi.

Ya kuma sake nanata kudurin KIRCT na ci gaba da gudanar da bincike mai tasiri da amfani.

Wakiliyar Rediyon Najeriya ta ruwaito  cewa an kafa Kano Independent Research Centre Trust(KIRCT) ne domin gudanar da bincike kan kiwon lafiya da cututtuka masu yaduwa da wadanda ba sa yaduwa, masu matukar muhimmanci ga lafiyar jama’a a Najeriya da ma fadin nahiyar Afirka.

 

Khadijah Aliyu

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati
  • Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
  • Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano