Leadership News Hausa:
2025-05-01@06:13:32 GMT

A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata

Published: 8th, February 2025 GMT

A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata

Wata ‘yar uwa ana auranta aka kira ta ana yi mata nasiha sai ta ce ni dai kun dame ni da na yi hakuri na yi hakuri, tun da yana sona ina son shi kam ai shike nan, wallahi ko shekara daya ba’a yi ba ran nan na kai mata ziyara sai take cewa Amina ashe da ake cewa na yi hakuri nake ganin an dame ni da gaskiyarsu yanzu wallahi har gani nake hakurin da aka ce na yi ma ya yi kadan.

To rayuwar aure sai da hakuri, idan muka yi hakurin nan da ake fada in sha Allahu za mu ga nasararsa a gaba, amma idan ba mu yi hakurin nan da ake fada mana ba za mu kasance cikin da na sani da damuwa a rayuwarmu. Saboda wasu da zarar auran fari za kufce musu sai ku ga ba za su taba samun nutsuwa ba, ko ga namiji ko macen wanda bai yi hakuri ba a cikin su. Wasu sai ku ga har karshe rayuwarsu ana nadama da da na sani.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike

Rahotonni sun tabbatar da cewa: Da tsakar daren jiya Litinin wayewar garin yau Talata, sojojin mamayar Isra’ila dauke da motocin soji guda hudu da wasu sojoji masu tafiyar kafa sun kutsa cikin yankunan kasar Siriya daga titin Al-Hurriya, inda suka wuce titin Al-Kassarat, zuwa Talat Jabata Al-Khashab.

Majiyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Siriya ta bayyana cewa: Sojojin mayar sun kafa shingen binciken ababen hawa inda suka tsaya suna binciken ababan hawa da ke wucewa, sannan suka haska wuta don gano hanyar kafin su fita ta hanyar da suka shiga. Jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila kuma suna shawagi a sararin samaniyar birnin Damascus fadar mulkin kasar ta Siriya.

A jiya Litinin ma, sojojin mamayar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wasu sansanoni na rundunar sojin ta 36 ta musamman da aka fi sani da Ain al-Burj a gabashin kauyen Qala’at Jandal da ke cikin karkarar birnin Damascus, tare da kafa wani sansanin soji a saman dutsen Barbar domin sa ido kan motsin da ake yi a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku