Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
Published: 14th, October 2025 GMT
“Idan mutum ya shiga jarrabawa kuma Allah Ya kawo dama ta afuwa, dole ne ya yi farin ciki. Ni da iyalina da masoyana mun yi murna ƙwarai,” in ji Lawan.
“Na gode wa Allah da kuma Shugaba Tinubu saboda ya yi abin da ya kamata a yaba masa.”
Ya bayyana cewa rayuwa a gidan yari ta koya masa juriya da fahimtar cewa komai ƙaddara ce.
“Tun kafin na bar kotu na sallama komai ga Allah. Na sani cewa duk inda mutum ya samu kansa, akwai darasi a ciki,” in ji shi.
Bayan fitowarsa daga gidan yari, Faruk Lawan ya sauya tafiyarsa ta siyasa.
Ya ce ya rabu da tafiyar Kwankwasiyya da aka san shi da ita, duk da cewa har yanzu yana yin zumunci da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.
“Shekara guda kenan da na fito daga gidan yari, amma akwai jigo a tafiyar Kwankwasiyya da bai taɓa kira ko taya ni murna ba,” in ji shi.
“A yanzu, siyasa ta faɗaɗa, jam’iyyar NNPP da muka shiga ta yi min ƙanƙanta, don haka dole mutum ya buɗe sabbin hanyoyi.”
Faruk Lawan ya ce yanzu yana son mayar da hankali kan siyasa ta ƙasa baki ɗaya, domin ya koyi cewa jarrabawa na nuna maka waye abokinka na gaskiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
Fitaccen malamin addinin Musulunci nan daga Jihar Bauchi, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya rasu.
Ɗansa, Sayyadi Ali Dahiru Usman Bauchi ne, ya tabbatar wa Aminiya rasuwar malamin.
Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban AmurkaYa ce sun karɓi wannan ƙaddara tare da gode wa Allah bisa rayuwar da malamin ya yi.
“Tabbas Sheikh ya koma ga Mahaliccinsa. Daga Allah muke, kuma gare Shi za mu koma,” in ji Sayyadi.
“Lokacin Sheikh ya yi. Mun gode wa Allah Maɗaukaki. Ya bai wa Sheikh tsawon rai, kuma rayuwarsa ta yi kyau. Alhamdulillah,” in ji shi.
Sayyadi, ya ce zuwa yanzu ba su yanke inda za a yi jana’izar malamin ba.