“Idan mutum ya shiga jarrabawa kuma Allah Ya kawo dama ta afuwa, dole ne ya yi farin ciki. Ni da iyalina da masoyana mun yi murna ƙwarai,” in ji Lawan.

“Na gode wa Allah da kuma Shugaba Tinubu saboda ya yi abin da ya kamata a yaba masa.”

Ya bayyana cewa rayuwa a gidan yari ta koya masa juriya da fahimtar cewa komai ƙaddara ce.

“Tun kafin na bar kotu na sallama komai ga Allah. Na sani cewa duk inda mutum ya samu kansa, akwai darasi a ciki,” in ji shi.

Bayan fitowarsa daga gidan yari, Faruk Lawan ya sauya tafiyarsa ta siyasa.

Ya ce ya rabu da tafiyar Kwankwasiyya da aka san shi da ita, duk da cewa har yanzu yana yin zumunci da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

“Shekara guda kenan da na fito daga gidan yari, amma akwai jigo a tafiyar Kwankwasiyya da bai taɓa kira ko taya ni murna ba,” in ji shi.

“A yanzu, siyasa ta faɗaɗa, jam’iyyar NNPP da muka shiga ta yi min ƙanƙanta, don haka dole mutum ya buɗe sabbin hanyoyi.”

Faruk Lawan ya ce yanzu yana son mayar da hankali kan siyasa ta ƙasa baki ɗaya, domin ya koyi cewa jarrabawa na nuna maka waye abokinka na gaskiya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026 October 13, 2025 Ilimi Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba October 13, 2025 Manyan Labarai Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano October 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa

Fitaccen malamin addinin Musulunci nan daga Jihar Bauchi, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya rasu.

Ɗansa, Sayyadi Ali Dahiru Usman Bauchi ne,  ya tabbatar wa Aminiya rasuwar malamin.

Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka

Ya ce sun karɓi wannan ƙaddara tare da gode wa Allah bisa rayuwar da malamin ya yi.

“Tabbas Sheikh ya koma ga Mahaliccinsa. Daga Allah muke, kuma gare Shi za mu koma,” in ji Sayyadi.

“Lokacin Sheikh ya yi. Mun gode wa Allah Maɗaukaki. Ya bai wa Sheikh tsawon rai, kuma rayuwarsa ta yi kyau. Alhamdulillah,” in ji shi.

Sayyadi, ya ce zuwa yanzu ba su yanke inda za a yi jana’izar malamin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran : Amurka Tasha Kashi A Yakin Kwanaki 12 Duk Da Manyan Makamai Na Zaman Da Take Da Su.
  • Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
  • Tarayyar Afirka ta yi Allah wadai da juyin mulkin da aka yi a Guinea-Bissau
  • ECOWAS ta yi Allah wadai da juyin mulki a Guinea Bissau
  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11