’Yan bindiga sun kashe mutum 4, sun sace 9 a Neja
Published: 2nd, October 2025 GMT
Aƙalla mutum huɗu suka rasu yayin da aka sace wasu tara a wani hari da ’yan bindiga suka kai a ƙauyuka da dama na Ƙaramar Hukumar Magama; ciki har da garin Ibeto a Jihar Neja.
Wani mazaunin yankin ya shaida wa Aminiya cewa mutum huɗu aka kashe, an jikkata wasu 11, sannan an yi garkuwa da mutum tara.
Rashin Tsaro: An rufe makarantu sama da 180 a Arewacin Najeriya Kwamitin Shura ya dakatar da Malam Lawan Triumph daga yin wa’azi a KanoDaga cikin waɗanda aka sace har da wanda ya wallafa rubutu a Facebook kan hare-haren ’yan bindiga a yankin, Barista Isyaku Muhammad Danjuma.
Rahotanni sun nuna cewa wasu masu bai wa ’yan bindiga bayanai ne suka sanar da su halin da ake ciki a yankin.
Mazauna yankin sun ce ’yan bindigar ɗauke da makamai sun kwana a Ibeto, inda suka dinga shiga gida-gida suna harbi tare da yin garkuwa da mutane.
Manoma da dama sun tsere daga gidajensu bayan harin, inda suka fantsama zuwa wasu ƙauyuka na Magama.
Hakazalika, ’yan bindigar sun sace shanun jama’a da dama daga daren ranar Talata zuwa ranar Laraba.
A wani bidiyo da ta karaɗe kafafen sada zumunta, an hangi maharan su suna kaɗa shanu daga garin Ibeto.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ci tura, domin bai ɗaga kiran waya ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari Ƙauyuka mahara yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya buƙaci al’umma su ƙara kula da tsaro tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, yayin da ’yan bindiga suka fara kai hare-hare a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina.
Sarkin, ya yi wannan kira ne yayin ziyarar jaje da ya kai wa al’ummar Faruruwa da ke Ƙaramar Hukumar Shanono a Jihar Kano.
Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16 Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — MuftwangA baya-bayan nan ’yan bindiga sun kai hari yankunan, inda suka sace shanu tare da yin garkuwa da mutane.
Sarki Sanusi, ya ce yawan hare-haren da ake fuskanta a yankin ya nuna cewa ana buƙatar kula da goyon bayan sarakunan gargajiya, gwamnati da kuma ƙungiyoyin sa-kai.
“Tsawon watanni da suka gabata, hare-hare sun ƙaru a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina, inda ’yan bindiga ke zuwa su sace shanu, su kashe jama’a, su yi garkuwa da maza da mata,” in ji shi.
Ya ce ya kai ziyarar ne domin jajanta wa mazauna yankin da abin ya shafa, tare da tabbatar musu da goyon bayan gwamnati, da kuma ƙarfafa musu gwiwa su taka rawa wajen kare ƙauyukansu.
“Nauyinmu ne a matsayinmu na shugabanni mu zo mu ga mutanenmu, mu yi musu ta’aziyya, mu kuma tabbatar musu cewa gwamnati da jami’an tsaro suna yin iya bakin ƙoƙarinsu,” ya ce.
Sarkin ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta tura jami’an tsaro da kayan aiki don tsaron yankin.
“Gwamna ya sayi motocin aiki, ya samar da kayan aiki, kuma mutane na gani da idonsu yadda sojoji da ’yan sanda ke yawan sintiri a yankin.
“Muna kuma ƙarfafa musu gwiwa su yi amfani da ’yan sa-kai wajen kare ƙauyukansu,” a cewarsa.
Sarki Sanusi, ya kuma bukaci al’ummomin Katsina da ke maƙwabtaka da yankunan da su tabbatar cewa yarjejeniyar sulhu da suke yi da ’yan bindiga ba za ta zama silar kawowa Kano hari ba.
Ya yi addu’ar Allah Ya wanzae da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa, tare da alƙawarin ci gaba da aiki tare da gwamnatin jihar domin kare rayukan jama’a.
“Muna rokon Allah Ya dawo mana da zaman lafiya, kuma za mu ci gaba da yin iya bakin ƙoƙarinmu tare da gwamnati domin tabbatar da tsaro a wannan jiha,” in ji shi.