NAPTIP ta Kama ‘Yan Safarar Mutane a Abuja, ta Kuɓutar da Mutane 24
Published: 2nd, October 2025 GMT
Hukumar da ke yaƙi da safarar mutane ta Nijeriya (NAPTIP) ta ce ta kama aƙalla mutum biyar da ake zargi da safarar mutane tare da kuɓutar da mutum 24 a filin jiragen saman ƙasa da ƙasa na Nnamdi Azikiwe International Airport, da ke Abuja.
Jami’in watsa labaran hukumar NAPTIP na ƙasa, Vincent Adekoye, ya bayyan a ranar Laraba cewa a cikin waɗanda aka kama akwai wani mutum da ya yi yunƙurin safarar ‘yarsa zuwa ƙasar Iraƙi.
Adekoye ya ce aikin, wanda aka yi bisa bayanan sirri da aka samu, ya samu jagorancin babbar daraktar hukumar, Binta Adamu Bello.
Adekoye ya ce aikin, wanda aka yi bisa bayanan sirri da aka samu, ya samu jagorancin babbar daraktar hukumar, Binta Adamu Bello.
Ya bayyana cewa a cikin waɗanda ake zargin akwai wani babban jami’in tsaro, wanda ke cikin masu safarar mutane a kudu maso yammacin Nijeriya.
Adekoye ya ce waɗanda aka kuɓutar ɗin yara ne da matasa waɗanda shekarunsu ke tsakanin shekara 15 zuwa 26 waɗanda aka ɗauko daga jihohin Kano da Katsina da Oyo da Ondo da kuma Ribas, kuma suna kan hanyarsu ta zuwa ƙasashen Iraƙi da Sudan da Masar da Saudiyya da Bahrain da kuma Afghanistan.
Ɗaya daga cikinsu ta sha alwashin cewa sai ta tabbatar an gurfanar da mahafinta a gaban kotu kan yunƙarin safararta da ya yi zuwa iraƙi, in ji jami’in.
Ya ƙara da cewa wata cikin waɗanda aka yi ƙoƙarin safarar ta ce mahafiyarta ce ta rinjaye ta ta yarda da cewa za ta tafi Turai domin yin aiki ta samu daloli.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yan Safara Hukumar Kuɓutarwa waɗanda aka
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta kama ƙunshi 66 na ganyen tabar wiwi a wani samame da ta kai a garin Deba, bayan samun wasu sahihin bayanan leƙen asiri.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:30 na dare a ranar 16 ga Nuwamba, 2025, lokacin da aka hango wata mota mara lamba, ƙirar Toyota Corolla, da ake zargi tana ɗauke da kayan, a kan hanyar Kuri zuwa Deba.
Hauhawar farashi ya ƙara raguwa a Nijeriya — NBS An ɗaura auren Sanata Kawu Sumaila da wata jami’ar soji a KanoAminiya ta ruwaito cewa, bayan isar jami’an wurin da ake zargin akwai kayan laifin ne, sun lura da wasu mutum uku suna ƙoƙarin yi wa wani mutum lodi a kan babur, lamarin da ya sanya ababen zargin suka tsere bayan hango ’yan sandan.
Binciken farko da aka gudanar ya kai ga gano buhuna uku ɗauke da ƙunshi 66 na ganyen da ake zargin tabar wiwi ce.
An dai kwashe kayayyakin zuwa ofishin ’yan sanda, kuma an fara bincike don kamo waɗanda suka tsere.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, ya jinjina wa jami’an da suka gudanar da wannan aiki, yana mai tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da fatattakar masu safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin jihar.