NAPTIP ta kama mahaifin da ke ƙoƙarin safarar ’yarsa zuwa Iraƙi ci-rani
Published: 2nd, October 2025 GMT
Hukumar Yaƙi da Safarar Mutane ta Ƙasa (NAPTIP) ta ce ta kama akalla mutane biyar da ake zargi da safarar mutane tare da ceto mutane 24 a Filin Jirgin Sama na Ƙasa Nnamdi Azikiwe, Abuja.
Hukumar ta ce daga cikin wadanda aka cafke ɗin, har da wani uba da ya yi ƙoƙarin safarar diyarsa zuwa Baghdad, babban birnin ƙasar Iraq.
Jami’in Yaɗa Labarai na NAPTIP, Vincent Adekoye, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.
Wannan na faruwa ne a daidai lokacin da ake ƙara nuna damuwa kan yawaitar safarar mutane, da kuma musamman waɗanda ke yin ƙaura suna barin ƙasar.
A cewar Adekoye, aikin da aka gudanar bayan samun sahihan bayanan sirri, Darakta Janar ta hukumar, Binta Adamu Bello ce ta jagorance shi.
Ya bayyana cewa cikin waɗanda aka kama akwai wani tsohon babban jami’in tsaro, wanda ake zargin babban mamba ne a cikin ƙungiyar masu safarar mutane a yankin Kudu maso Yammacin Najeriya.
Sanarwar ta ce, “A wani babban farmaki da ba a taɓa yin irinsa ba, wanda ya zo ba tare da an shirya ba, Darakta Janar na Hukumar Hana Safarar Mutane ta Ƙasa, Binta Adamu Bello, a yau (Laraba) ta jagoranci wani babban aiki na musamman a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, wanda ya kai ga ceto mutane 24 da ake ƙoƙarin yin safararsu da kuma kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane.”
“Cikin waɗanda aka kama a filin jirgin sama akwai wani tsohon jami’in tsaro daga ɗaya daga cikin manyan hukumomin tsaro na Najeriya, wanda ake zargin babban mamba ne a cikin ƙungiyar masu safarar mutane a yankin Kudu maso Yamma.”
“Aikin da aka tsara sosai, wanda sauran matafiya a filin jirgin suka yaba da shi, ci gaba ne da sabon shirin yaki da safarar mutane da Darakta Janar ta ƙaddamar, wanda ke nufin kai farmaki ga wuraren ɗaukar mutane, wuraren safara da hanyoyin da ake bi a cikin Najeriya.”
Adekoye ya ce waɗanda aka ceto matasa ne masu shekaru tsakanin 15 zuwa 26, waɗanda aka ɗauko daga jihohin Kano, Katsina, Oyo, Ondo da Ribas, kuma suna kan hanyarsu ne ta zuwa kasashen Iraq, Sudan, Masar, Saudiyya, Bahrain da Afghanistan.
Yayin da yake ambato daga cikin waɗanda aka ceto, Adekoye ya ce ɗaya daga cikinsu ta sha alwashin ganin mahaifinta ya fuskanci hukunci saboda ƙoƙarin safararta zuwa Iraq.
Ya ƙara da cewa wata daga cikin waɗanda aka ceto ta bayyana cewa an yaudari mahaifiyarta da cewa za ta je Turai don yin aiki da samun kuɗaɗe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iraq cikin waɗanda aka da safarar mutane
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu
Jam’iyyar PDP ta kori Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da tsohon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Samuel Anyanwu.
PDP ta yanke wannan hukunci ne a babban taron jam’iyyar da ake gudanarwa a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.
Gwamnati, UNICEF da ’yan jarida sun haɗa don yaƙar cututtukan da aka manta da su a Gombe Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — KwankwasoTsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na yankin Kudu, Cif Olabode George ne, ya gabatar da ƙudirin korarsu, sannan Samaila Burga, shugaban PDP na Jihar Bauchi, ya mara masa baya.
A baya, tsagin jam’iyyar da ke goyon bayan Wike sun kai ƙara kotu don a hana gudanar da taron.
Amma PDP ta samu hukuncin da ya ba ta damar ci gaba da taron daga Kotun Ƙoli ta Jihar Oyo.
Kwana biyu kafin taron, Mao Ohuabunwa, Shugaban Majalisar Amintattu (BoT) na ɓangaren Wike, ya ce duk wanda ya tafi Ibadan don taron hutu ya je yi, domin doka ba za ta aminta da shi ba.
A cewarsa, Anyanwu ya riga ya fitar da sanarwar ɗage taron.
Ohuabunwa ya ce: “Mun zauna a matsayin kwamitin zartarwa na ƙasa na PDP, muka duba abubuwan da muka yi. Mun yadda da bin hukuncin kotu game da taron Ibadan. Don haka ba mu da hannu a taron.
“Ibadan wurin jama’a ne, mutane na iya zuwa don kowane abu amma ba don babban taro ba. Duk wanda ya tafi can da sunan taro ya ɗauki hakan a matsayin shaƙatawa kawai.
“Ba za mu amince da take haƙƙin kundin tsarin mulki da wasu mutanen ke yi da sunan babban taro ba.”
Muƙaddashin shugaban tsagin, Abdulrahman Muhammad, shi ma ya kira wakilansu da su guji zuwa taron.
Ya ce tsagin nasu zai ci gaba da haɗa kan mambobi a jihohi 36 da Abuja domin ƙarfafa jam’iyyar.
Muhammad ya ce: “Muna kiran dukkanin wakilai su guji zuwa taron Ibadan.”
A nasa jawabin, Wike ya gode wa mambobin jam’iyyar saboda yadda suke tsayawa wajen kare jam’iyyar a yankunansu.
Ya ce su a ɓangarensu za su ci gaba da bin doka kuma ba za su bari a tsoratar da su ba.
Wike, ya kuma ce ba zai taɓa yaudarar waɗanda ke goyon bayan kundin tsarin mulkin jam’iyyar ba.
Ya ce: “Ina farin ciki da yadda kuke nuna damuwa game da jam’iyyar a yankunanku. Zan ci gaba da goyon bayanku, ba zan yaudare ku ba.”