Aminiya:
2025-11-18@14:04:48 GMT

PENGASSAN ta dakatar da yajin aiki, ta gargaɗi matatar Dangote

Published: 1st, October 2025 GMT

Ƙungiyar Ma’aikata Masu Aikin Mai da Gas (PENGASSAN), ta dakatar da yajin aikin kwanaki uku da ta fara biyo bayan rikici tsakaninta da matatar Dangote.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne a wani taron manema labarai da ta gudanar a ranar Laraba.

Hatsarin Jirgin Ruwa: Adadin waɗanda suka rasu ya kai 26 a Kogi Jihar Gombe ta fara aiwatar da dokar hana kiwo da daddare

Ƙungiyar ta kuma gargaɗi matatar Dangote da kada ta kaeya yarjejeniyar da aka cimma a ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro.

Shugaban PENGASSAN, Festus Osifo, wanda ya sanar da janye yajin aikin, ya ce idan matatar ta karya yarjejeniyar, ƙungiyar ba za ta yi shiru ba.

Rikicin ya samo asali ne bayan wasu ma’aikatan matatar Dangote sun shiga ƙungiyar PENGASSAN, lamarin da ya haddasa rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu.

Yajin aikin ƙungiyar ya haifar da tsoron samun ƙarancin man fetur da gas a faɗin Najeriya.

Har ila yau, ƙungiyar ta yi barazanar daina kai wa matatar Dangote mai, lamarin da ka iya zama babbar barazana ga harkar man fetur a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargaɗi Matatar Dangote Yajin aiki matatar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Taraba, Rt Hon. Kizito Bonzena, tare da ’yan majalisar 15 sun sauya sheka daga jam’iyyarsu ta PDP zuwa APC.

A saifyar Litinin ne Rt Hon. Kizito Bonzena ya gabatar da takardarsa ta ficewa daga PDP tare da sauran mambobin zuwa APC.

Ya bayyana cewa da sauyin shekar tasu, yanzu APC ce ke da daukacin kujeru 24 da ke Majalisar Dokokin Jihar Taraba.

Hakan na zuwa ne jim kadan bayan Gwamnan Jihar Taraba, Kefas ya sanar da shirinsa na komawa APC daga PDP.

Masu ibadar Umarah 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka ’Yan ta’adda sun sace dalibai 25 a dakunan kwanansu a Kebbi

Sauran mambobin majalisar da suka sauya sheka sun hada da Mataimakin Shugaban Malisar, Hamman Adama Abdullai (Bali 2) da Shugaban Masu Rinjaye, Jethro Yakubu (Wukari 1). Sauran sun hada da Tafarki Eneme (Kurmi ); Akila Nuhu (Lau ); Musa Chul (Gassol 1);  da Josiah Yaro (Wukari 2).

Akwai kuma Tanko Yusuf (Takum 1), Veronica Alhassan (Bali 1), Anas Shuaibu (Karim Lamido 2), Nelson Len (Nguroje), Umar Adamu (Jalingo 1), Joseph Kassong (Yorro), John Lamba (Takum 2), Happy Shonruba (Ardo-Kola) da kuma Zakari Sanusi (Ibi Constituency).

Da yake sanar da sauyin shekar tasu, shugaban majalisar ya bayyana cewa sun yi hakan ne saboda bukatar al’umma ba don bukatar kansu ba.

Tsohon Shugaan Malisar Dokokin Jihar, Peter Diah, ya yi maraba da su a APC.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji
  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • ’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC
  • Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa
  • Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca
  • Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 
  •  An Bayyana Sunayen Kasashen Da Su Fi Sayarwa “Isra’ila” Man Fetur A Lokacin Yakin Gaza