‘PENGASSAN ta amince ta janye yajin aiki kan rikincinta da matatar Dangote’
Published: 1st, October 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta ce Kungiyar Ma’aikatan Harkokin Man Fetur da Gas ta Najeriya (PENGASSAN) ta amince da janye yajin aikin da take yi, bayan zaman sulhun kwanaki biyu da aka gudanar tare da shugabannin matatar man Dangote.
Zaman sulhun da aka gudanar a ranakun 29 da 30 ga Satumba, 2025, ya gudana ne a karkashin jagorancin Ministan Kwadago da samar da Ayyukan Yi, Dr.
A cikin sanarwar da aka fitar bayan kammala zaman, Minista Dingyadi ya ce yajin aikin na PENGASSAN ya biyo bayan sallamar ma’aikata sama da 800 daga matatar man Dangote.
Ministan ya ce, “Shugabannin PENGASSAN sun bayyana cewa umarnin dakatar da samar da gas ga kamfanin Dangote da kuma janye ayyuka ya biyo bayan sallamar sama da mambobi 800”.
A nasa bangaren, shugabancin kamfanin na Dangote, ya ce sallamar ma’aikatan ya faru ne sakamakon “gyare-gyaren da ake gudanarwa a cikin kamfanin.”
Bayan doguwar tattaunawa, bangarorin biyu sun cimma matsaya.
A cewar Ministan, “shugabancin kamfanin Dangote zai fara daukar matakin mayar da ma’aikatan da aka sallama zuwa wasu kamfanoni da ke karkashin rukunin kamfanoninsa ba tare da sun rasa albashinsu ba.”
Sanarwar ta kuma jaddada cewa ba za a ci zarafin kowanne ma’aikaci ba saboda rawar da ya taka a cikin rikicin.
Dangane da hakkokin kungiyoyin kwadago, Dingyadi ya tabbatar da cewa “yin kungiya hakki ne na ma’aikata bisa dokokin Najeriya, kuma dole ne a mutunta wannan hakki.”
Ya kara da cewa PENGASSAN ta amince ta fara aiwatar da janye yajin aikin da zuciya daya
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
Gobara ta laƙume rayukan wasu yara biyu ’yan gida ɗaya a unguwar Rumuola da ke ƙaramar hukumar Obio/Akpor a Jihar Ribas.
Bayanai sun ce ibtila’in ya auku ne da misalin ƙarfe 10 na dare a ranar Lahadi, lokacin da gobarar ta tashi a ɗaya daga cikin wasu ɗakunan haya da mahaifiyar yaran ta kulle ’ya’yanta huɗu ta tafi sayen kayan girki.
Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno ’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a GombeA cewar mazauna yankin, cikin yaran huɗun, biyun da suka riga suka kwanta barci sun ƙone su kurmus, yayin da sauran biyun da ke farke suka samu damar tserewa.
Aminiya ta ruwaito cewa, mazauna yankin da sun ankara da gobarar ce bayan sun hangi yadda hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya, lamarin da ya sa suka gaggauta kiran ma’aikatar kashe gobara kuma suka kawo dauki domin tarar hanzarin lamarin na hana gobarar bazuwa zuwa sauran gidaje.
Haka kuma, wani mazaunin yankin ya musanta jita-jitar da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa gobarar ta tashi ne a harabar wata kwaleji ta Captain Elechi Amadi da ke Rumuola, yana mai bayyyan cewa lamarin ya faru ne a bayan makarantar, inda ake da dogayen gine-gine da ke ɗauke da iyalai sama da 27.
Ya bayyana takaicin cewa dubban mutane sun rasa matsugunni a sanadiyar gobarar wadda ta ƙone dukiyoyin da darajarsu ta kai miliyoyin naira.
Mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa yaran biyu da suka mutu shekarunsu na haihuwa ba su gaza biyar da tara ba.
Ta ce an fara bincike domin gano musabbabin gobarar, kana an gayyaci mahaifiyar yaran domin amsa tambayoyi.