An kuma amince da cewa ma’aikatan da aka kora za a mayar da su kan ayyukan su cikin wasu kamfanoni na rukunin Dangote ba tare da sun yi asarar albashi ba, kuma babu wani ma’aikaci da za a ci zarafinsa saboda rawar da ya taka a wannan taƙaddamar.

 

 

An cimma matsayar ne a gaban manyan jami’an gwamnati da suka hada da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ministan kudi kuma mai kula da tattalin arziki, ministan kasafin kudi da tsare-tsare, karamin ministan albarkatun man fetur (Gas) da shugabannin NMDPRA da NUPRC, da wakilan kamfanin man fetur na kasa (NNPCL).

 

Haka kuma shugabannin kungiyar ‘yan kasuwa (TUC) sun halarci tattaunawar tare da shugabannin kungiyar ta PENGASSAN da kuma mahukuntan matatar Dangote.

 

Idan dai za a iya tunawa dai rikicin ya samo asali ne bayan da matatar man ta Dangote ta kori mambobin kungiyar ta PENGASSAN sama da 800, lamarin da ya sa kungiyar ta fitar da umarnin dakatar da samar da iskar gas ga matatar ta kuma janye ayyukanta a fadin kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce gwamnati ce ke da alhakin samar da tsaro da haɗin kai a Jihar Filato da kuma Najeriya baki ɗaya.

Ya ce babu wata ƙasa da za ta shigo don kawo zaman lafiya na dindindin a Najeriya, face ’yan ƙasa sun haɗa kai.

’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang

Akpabio, ya yi wannan magana ne a filin Polo na Jos a ranar Asabar yayin taron tarbar sabbin mambobin da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a Jihar Filato.

Ya kira jama’a da su goyi bayan ƙoƙarin samar da zaman lafiya tare da yin aiki don ƙarshen rikice-rikece.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu yana ƙoƙarin kawo ƙarshen kashe-kashe da tabbatar da zaman lafiya a Filato da sauran sassan ƙasar nan.

“Muna roƙon Allah Ya taimaka mana mu samu zaman lafiya a Filato. Duk wanda zai mulki Filato dole ne ya zama mutum mai kishin zaman lafiya. Wannan ita ce jam’iyyar da ta ke kula da ku,” in ji shi.

Akpabio, ya ƙara da cewa: “Na zo a madadin Shugaban Ƙasa domin tabbatar muku cewa za mu yi duk abin da ya kamata domin ku samu zaman lafiya.

“Babu wasu mutane daga waje da za su zo su kawo muku zaman lafiya. Dole mu ne za mu samar da shi. Dole mu zauna lafiya da juna. Najeriya na buƙatar zaman lafiya domin samun ci gaba.”

Ya tabbatar wa al’ummar Jihar Filato cewa gwamnati za ta magance matsalolin da suke fuskanta.

“Ina kuka a duk lokacin da na ji an kashe wani mutum; yaro ko babba. Matsalar da muke fuskanta ba yau ta samo asali ba.

“Mutane da dama sun mutu a Filato. An zubar da jini mai yawa, kuma ba mu farin ciki da haka. Shugaban Ƙasa ma ba ya farin ciki,” in ji shi.

Akpabio ya amince cewa da cewar ana kashe-kashe, tashe-tashen hankula a ƙasar nan, amma ya yi alƙawarin cewa nan da wani lokaci lamarin zai zama tarihi.

Ya roƙi al’ummar Filato da su goyi bayan Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewar za su samar da ci gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Shugaban Iran Na Daya Ya Gana Da Prime Ministan Rasha A Birnin Mosko
  • Ministan tsaron Iran na Ziyara a UAE don karfafa dangantakar tsaro tsakanin kasashen yankin
  • MDD ta amince da kudurin tura dakarun kasa da kasa zuwa Gaza
  • Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty
  • Aref: Iran Tana Da Kyakkyawar Alaka Da Mambobin Kungiyar Hadin Gwiwa Ta Shanghai {SCO}
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • DRC: An Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar M23
  •  An Amince Da  Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA