Aminiya:
2025-11-18@11:02:18 GMT

Gwamna Abba ya bukaci Tinubu ya cire Kwamishinan ’Yan Sandan Kano

Published: 1st, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Shugaban Kasa Bola Tinubu ya cire Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori, saboda yadda ya siyasantar da aikinsa.

Kiran na zuwa ne bayan kwamishinan tare da ilahirin dakarun rundunar a jihar sun kaurace wa halartar bikin tunawa da ranar samun ’yancin kai da aka gudanar a jihar.

A bisa al’ada dai Gwamna kan jagoranci hukumomin tsaro wajen gudanar da faretin bikin ranar a duk ranar daya ga watan Oktoba. To sai dai a bana, ba a ga Kwamishinan ’Yan Sandan na Kano ba, sannan babu ko dan sanda daya a wajen bikin.

Bayan wuya sai daɗi: Sakon Tinubu ga ’yan Najeriya Sojoji sun kama ’yan sandan bogi da motoci 2 makare da tabar wiwi a Taraba

Da yake jawabi a wajen taron da ya gudana a filin was ana Sani Abacha da ke Kano ranar Laraba, gwamnan ya bayyana rashin jin daɗinsa kan wannan mataki, yana mai cewa hakan cin mutunci ne ga al’ummar Kano da kuma ruhin haɗin kan ƙasa.

Gwamnan ya ce, “A ƙarshen jawabina, ina kira ga dukkan hukumomin tsaro da su ci gaba da sadaukar da kansu wajen tabbatar da zaman lafiya a jihohin ƙasar nan, ciki har da Kano. Amma musamman hukumomin tsaro a Kano, bai kamata su tsoma kansu cikin siyasar bangaranci ba, domin hakan ba zai amfani kowa ba a Kano da ma Najeriya ba.

“Ina so in yi amfani da wannan dama a matsayina na ɗan Najeriya, ɗan Kano, kuma Babban jami’in tsaron Jihar Kano, in yi alla-wadai da halin rashin ƙwarewa da nuna bangaranci da Kwamishinan ’Yan Sanda na yanzu ke nunawa,” in ji gwamnan.

Gwamna Yusuf ya ce rashin halartar Kwamishinan da jami’ansa a bikin wani mataki ne da aka yi da gangan, kuma ya ce hakan ya jawo wa jihar kunya a rana mai tarihi.

“Kamar yadda kuke gani, a wannan rana ta tarihi ta bikin ’yancin kai na Najeriya, ya yanke shawarar ya janye daga jerin faretin tare da jami’ansa. Wannan mataki ne da ya shafe shi da mutanensa. A matsayina na Babban Jami’in Tsaro na Kano, a madadin gwamnati, ba mu ji dadin wannan hali da Kwamishinan ’Yan Sanda ya nuna ba,” in ji shi.

Gwamnan ya jaddada cewa Kano na cikin zaman lafiya, kuma al’ummar jihar sun dade suna jiran wannan rana don su taru su yi murnar ’yancin ƙasa tare.

Ya kuma ce matakin na Kwamishinan ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya.

Gwamnan ya bayyana halin Kwamishinan da kalmomin “rashin ƙwarewa,” “rashin da’a,” da “rashin yin biyayya ga kasa.”

A ƙarshe, yayin da yake godewa sauran hukumomin tsaro da suka halarta, Gwamna Yusuf ya tabbatar da goyon bayan gwamnatinsa wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a Kano da Najeriya baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwamishan Yan Sanda hukumomin tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

PDP za ta sake farɗaɗowa idan shugabanninta suka cire girman kai — Anenih

Tsohuwar Shugabar Mata ta Jam’iyyar PDP, Iyom Josephine Anenih, ta ce jam’iyyar za ta sake yin ƙarfi idan shugabanninta suka cire girman kai suka mayar da hankali kan yi wa jama’a hidima.

Ta bayyana haka ne yayin babban taron PDP da aka gudanar a Ibadan a ranar Asabar.

PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso

Ta ce har yanzu ’yan Najeriya da dama suna sa ran jam’iyyar za ta sake yin ƙarfi domin yi musu jagoranci.

Anenih, ta yi gargaɗin cewa PDP na iya zama tarihi idan ba a gyara matsalolinta ba.

“Idan ba mu fuskanci matsalolinmu ba, PDP za ta zama tarihi, labarin yadda sakaci da girman kai suka lalata babbar jam’iyyar siyasa mafi girma a Afirka,” in ji ta.

Ta ƙara da cewa rikicin cikin gida, rashin ladabi, da cin amanar juna ne suka raunana jam’iyyar.

“Mambobinmu su ne ƙarfin PDP na gaskiya. Sun yi tsayin daka duk da matsalolin da ake fuskanta. Wannan babban taro dole ne ya girmama jajircewarsu,” ta ce.

Anenih, ta roƙi shugabannin jam’iyyar su kawo ƙarshen rigingimu da suka dabaibaye ta hanyar haɗa kai don sake gina jam’iyyar.

Ta ce Najeriya na buƙatar jam’iyyar adawa mai ƙarfi, wacce za ta kawo ƙarshen talauci da rashin tsaro da ake fama da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu shigar da kara na ICC sun bukaci hukuncin daurin rai da rai a kan kwamandan RSF
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • PDP za ta sake farɗaɗowa idan shugabanninta suka cire girman kai — Anenih
  • Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso
  • Sanusi ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso
  • Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano